< 1 Tarihi 15 >

1 Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
David si je v Davidovem mestu zgradil hiše in pripravil kraj za Božjo skrinjo in zanjo razpel šotor.
2 Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
Potem je David rekel: »Božje skrinje ne bi smel nositi nihče razen Lévijevcev, kajti njih je Gospod izbral, da nosijo Božjo skrinjo in da mu služijo na veke.«
3 Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
David je skupaj zbral ves Izrael v Jeruzalemu, da prinese gor Gospodovo skrinjo na kraj, ki ga je pripravil zanjo.
4 Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
David je zbral Aronove otroke in Lévijevce.
5 Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
Izmed Kehátovih sinov vodja Uriéla in sto dvajset njegovih bratov;
6 daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
izmed Meraríjevih sinov vodja Asajája in dvesto dvajset njegovih bratov;
7 daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
izmed Geršómovih sinov vodja Joéla in sto trideset njegovih bratov;
8 daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
izmed Elicafánovih sinov vodja Šemajá in dvesto njegovih bratov;
9 daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
izmed Hebrónovih sinov vodja Eliéla in osemdeset njegovih bratov;
10 daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
izmed Uziélovih sinov vodja Aminadába in sto dvanajst njegovih bratov.
11 Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
David je dal poklicati Cadóka, duhovnika Abjatárja in Lévijevce Uriéla, Asajá, Joéla, Šemajá, Eliéla in Aminadába
12 Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
ter jim rekel: »Vi ste vodje očetov Lévijevcev. Posvetite se tako vi kakor vaši bratje, da boste lahko prinesli gor skrinjo Gospoda, Izraelovega Boga, na kraj, ki sem ga pripravil zanjo.
13 Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
Kajti ker tega niste najprej storili, je Gospod, naš Bog, nad nami naredil vrzel, ker ga nismo iskali po predpisanem redu.«
14 Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Tako so se duhovniki in Lévijevci posvetili, da prinesejo gor skrinjo Gospoda, Izraelovega Boga.
15 Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
Lévijevi otroci so na svojih ramenih nosili Božjo skrinjo z njenima drogovoma v njej, kakor je zapovedal Mojzes, glede na Gospodovo besedo.
16 Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
David je spregovoril vodju Lévijevcev, da določi svoje brate, da bodo pevci z glasbenimi instrumenti, plunkami, harfami in cimbalami, z dvigovanjem zvenečega radostnega glasu.
17 Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
Tako so Lévijevci določili Joélovega sina Hemána in izmed njegovih bratov Berehjájevega sina Asáfa in izmed Meraríjevih sinov, njihovih bratov, Kušajájevega sina Etána
18 Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
in z njimi njihove brate druge stopnje: Zeharjája, Bena, Jaaziéla, Šemiramóta, Jehiéla, Uníja, Eliába, Benajája, Maasejája, Matitjája, Elifeléhuja, Miknejája, Obéd Edóma in Jeiéla, vratarje.
19 Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
Tako so bili pevci Hemán, Asáf in Etán določeni, da igrajo na cimbale iz brona,
20 Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
Zeharjá, Jaaziél, Šemiramót, Jehiél, Uní, Eliáb, Maasejá in Benajá s plunkami na sopran,
21 Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
in Matitjá, Elifeléhu, Miknejá, Obéd Edóm, Jeiél in Azazjá s harfami v oktavi, da vodijo.
22 Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
Kenanjá, vodja Lévijevcev, je bil za pesem. Poučil je glede pesmi, ker je bil vešč.
23 Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
Berehjá in Elkaná sta bila vratarja za skrinjo.
24 Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
Duhovniki Šebanjá, Józafat, Netanél, Amasáj, Zeharjá, Benajá in Eliézer so s trobentami trobili pred Božjo skrinjo; Obéd Edóm in Jehijá pa sta bila vratarja za skrinjo.
25 Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
Tako so David, Izraelove starešine in tisočniki odšli, da iz hiše Obéd Edóma z radostjo prinesejo gor Gospodovo skrinjo zaveze.
26 Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
Pripetilo se je, ko je Bog pomagal Lévijevcem, da so nosili skrinjo Gospodove zaveze, da so darovali sedem bikcev in sedem ovnov.
27 To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
David je bil oblečen s svečanim oblačilom iz tankega lanenega platna in vsi Lévijevci, ki so nosili skrinjo, pevci in Kenanjá, mojster pesmi s pevci; tudi David je imel na sebi efód iz lana.
28 Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
Tako je ves Izrael prinesel gor Gospodovo skrinjo zaveze z vriskanjem, z zvokom kornéta, s trobentami, cimbalami in igrali so s plunkami in harfami.
29 Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.
Pripetilo se je, medtem ko je Gospodova skrinja prišla v Davidovo mesto, da je Savlova hči Mihála, zroč skozi okno, videla kralja Davida plesati in igrati in ga v svojem srcu prezirala.

< 1 Tarihi 15 >