< 1 Tarihi 15 >

1 Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
HANA iho la ia i na hale nona maloko o ke kulanakauhale o Davida, a hoomakaukau iho la hoi oia i wahi no ka pahu o ke Akua, a kukulu iho la i halelewa nona.
2 Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
Alaila, olelo mai la o Davida, Aohe mea e ae nana e amo i ka pahu o ke Akua, o na Levi wale; no: no ka mea, ua koho o Iehova ia lakou e amo i ka pahu o ke Akua, a e lawelawe nana a mau loa no.
3 Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
Houluulu mai la o Davida i ka Iseraela a pau i Ierusalema, e lawe mai i ka Pahu o Iehova i kona wahi, kahi ana i hoomakaukau ai nona.
4 Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
Houluulu ae la o Davida i na mamo a Aarona, a me na Levi:
5 Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
O na mamo a Kohata; o Uriela ka luna, a o kona poe hoahanau hookahi haneri a me ka iwakalua:
6 daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
O na mamo a Merari; o Asaia ka luna, a o kona poe hoahanau he elua haneri a me ka iwakalua:
7 daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
O na mamo a Geresoma; o Ioela ka luna, a o kona poe hoahanau he haneri a me ke kanakolu;
8 daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
O na mamo a Elizapana; o Semaia ka luna, a o kona poe hoahanau he elua haneri:
9 daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
O na mamo a Heberona; o Eliela ka luna, a o kona poe hoahanau he kanawalu:
10 daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
O na keikikane a Uziela; o Aminadaba ka luna, a o kona poe hoahanau he haneri a me ka umikumamalua.
11 Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
Kahea aku la o Davida ia Zadoka laua o Abiatara na kahuna, a i na Levi hoi, ia Uriela, Asaia, Ioela, Semaia, Eliela, a me Aminadaba,
12 Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
I aku la oia ia lakou, O oukou na luna ohana o na Levi; e huikala ia oukou iho, oukou a me na hoahanau o oukou, i lawe mai ai oukou i ka pahu o Iehova ke Akua o ka Iseraela i kahi a'u i hoomakaukau ai nona.
13 Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
No ka mea, no ka oukou hana ole ana ia me. mamua, i hookae mai ai o Iehova ko kakou Akua maluna o kakou, no ko kakou imi ole ana ia ia ma ka pololei maoli.
14 Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Nolaila, i huikala ai na kahuna a me na Levi ia lakou iho, i mea e lawe mai ai i ka pahu o Iehova ke Akua o ka Iseraela.
15 Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
A amo mai la na mamo a Levi i ka pahu o ke Akua maluna o ko lakou poohiwi, ma na auamo o luna, me ka Mose i kauoha mai ai, e like me ka olelo a Iehova.
16 Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
Olelo mai la o Davida i na luna o na Levi, e hoonoho i ko lakou poe hoahanau, i poe hoolea, me na mea kani, na pesaleteria, na lira, na kimebala, e hookani ana me ka hookiekie ana i ka leo me ka olioli.
17 Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
A hoonoho aku la na Levi ia Hemana ke keiki a Ioela; a no kona poe hoahanau, ia Asapa ke keiki a Berekia; a no na mamo a Merari o ko lakou poe hoahanau, o Etana ke keiki a Kusaia;
18 Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
A me lakou pu ko lakou mau hoahanau mamuli iho, o Zekaria, o Bena, o Iaaziela, o Semiramota, o Iehiela, o Uni o Eliaba, o Benaia, o Maaseia, o Matitia, o Elipele, o Mikeneia, o Obededoma, a o Ieiala na kiaipuka.
19 Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
Pela na mea hoolea, o Hemana, o Asapa, a o Etana, e hookani lakou me na kimebala keleawe:
20 Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
A o Zekaria, o Aziela, o Semiramota, o Iehiela, o Uni, o Eliaba, o Maaseia, a o Benaia, me na pesaleteria ma ka Ieo kiekie;
21 Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
A o Matitia, o Elipele, o Mikeneia, o Obededoma, o Ieiela, o Azazia, me na lira ma ka leo haahaa e alakai ai.
22 Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
A o Kenania, ka luna o ka Levi, no ka leo mele no ia; ao aku la ia i ka leomele, no ka mea, he akamai kona.
23 Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
A o Berekia laua o Elekana na kiaipuka no ka pahu.
24 Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
A o Sebenia, o Iehosapata, o Netaneela, o Amasai, o Zekerta, o Benaia, a o Eliezera, na kahuna i puhi i na pu imua o ka pahu o ke Akua: a o Obededoma laua o Iehia na kiaipuka no ka pahu.
25 Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
Pela o Davida me na lunakahiko o ka Iseraela a me na luna tausani i hele aku ai, e lawe mai i ka pahuberita o Iehova, mai ka hale o Obededoma mai me ka olioli.
26 Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
A i ka manawa a ke Akua i kokua mai ai i na Levi e amo ana i ka pahuberita o Iehova, alaila mohai aku la lakou i na bipikane ehiku, a me na hipakane ehiku.
27 To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
Ua aahuia o Davida i ka aahu makue, a me na Levi e amo ana i ka pahu a me ka poe memele, a o Kenania ke kumu ao i ka mele, a me ka poe memele: maluna hoi o Davida kekahi epoda olona.
28 Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
Pela ka Iseraela a pau i lawe mai ai i ka pahuberita o Iehova me ka hooho ana, a me ke kani ana o ke koreneta, a o na pu, a mo na kimebala, e hookani ana hoi i na pesaleteria a me na lira.
29 Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.
A hiki mai la ka pahuberita o Iehova i ke kulanakauhale o Davida, nana mai la o Mikala ke kaikamahine a Saula ma ka pukamakani, a ike mai la i ke alii ia Davida e haa ana a e hookani ana: hoowahawaha iho la oia ia ia maloko o kona naau.

< 1 Tarihi 15 >