< 1 Tarihi 15 >
1 Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
David se bâtit des maisons dans la cité de David; il prépara une place à l’arche de Dieu, et dressa pour elle une tente.
2 Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
Alors David dit: L’arche de Dieu ne doit être portée que par les Lévites, car l’Éternel les a choisis pour porter l’arche de Dieu et pour en faire le service à toujours.
3 Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
Et David assembla tout Israël à Jérusalem pour faire monter l’arche de l’Éternel à la place qu’il lui avait préparée.
4 Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
David assembla les fils d’Aaron et les Lévites:
5 Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
des fils de Kehath, Uriel le chef et ses frères, cent vingt;
6 daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
des fils de Merari, Asaja le chef et ses frères, deux cent vingt;
7 daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
des fils de Guerschom, Joël le chef et ses frères, cent trente;
8 daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
des fils d’Élitsaphan, Schemaeja le chef et ses frères, deux cents;
9 daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
des fils d’Hébron, Éliel le chef et ses frères, quatre-vingts;
10 daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
des fils d’Uziel, Amminadab le chef et ses frères, cent douze.
11 Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
David appela les sacrificateurs Tsadok et Abiathar, et les Lévites Uriel, Asaja, Joël, Schemaeja, Éliel et Amminadab.
12 Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
Il leur dit: Vous êtes les chefs de famille des Lévites; sanctifiez-vous, vous et vos frères, et faites monter à la place que je lui ai préparée l’arche de l’Éternel, du Dieu d’Israël.
13 Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
Parce que vous n’y étiez pas la première fois, l’Éternel, notre Dieu, nous a frappés; car nous ne l’avons pas cherché selon la loi.
14 Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Les sacrificateurs et les Lévites se sanctifièrent pour faire monter l’arche de l’Éternel, du Dieu d’Israël.
15 Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
Les fils des Lévites portèrent l’arche de Dieu sur leurs épaules avec des barres, comme Moïse l’avait ordonné d’après la parole de l’Éternel.
16 Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
Et David dit aux chefs des Lévites de disposer leurs frères les chantres avec des instruments de musique, des luths, des harpes et des cymbales, qu’ils devaient faire retentir de sons éclatants en signe de réjouissance.
17 Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
Les Lévites disposèrent Héman, fils de Joël; parmi ses frères, Asaph, fils de Bérékia; et parmi les fils de Merari, leurs frères, Éthan, fils de Kuschaja;
18 Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
puis avec eux leurs frères du second ordre Zacharie, Ben, Jaaziel, Schemiramoth, Jehiel, Unni, Éliab, Benaja, Maaséja, Matthithia, Éliphelé et Miknéja, et Obed-Édom et Jeïel, les portiers.
19 Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
Les chantres Héman, Asaph et Éthan avaient des cymbales d’airain, pour les faire retentir.
20 Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
Zacharie, Aziel, Schemiramoth, Jehiel, Unni, Éliab, Maaséja et Benaja avaient des luths sur alamoth;
21 Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
et Matthithia, Éliphelé, Miknéja, Obed-Édom, Jeïel et Azazia, avaient des harpes à huit cordes, pour conduire le chant.
22 Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
Kenania, chef de musique parmi les Lévites, dirigeait la musique, car il était habile.
23 Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
Bérékia et Elkana étaient portiers de l’arche.
24 Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
Schebania, Josaphat, Nethaneel, Amasaï, Zacharie, Benaja et Éliézer, les sacrificateurs, sonnaient des trompettes devant l’arche de Dieu. Obed-Édom et Jechija étaient portiers de l’arche.
25 Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
David, les anciens d’Israël, et les chefs de milliers se mirent en route pour faire monter l’arche de l’alliance de l’Éternel depuis la maison d’Obed-Édom, au milieu des réjouissances.
26 Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
Ce fut avec l’assistance de Dieu que les Lévites portèrent l’arche de l’alliance de l’Éternel; et l’on sacrifia sept taureaux et sept béliers.
27 To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
David était revêtu d’un manteau de byssus; il en était de même de tous les Lévites qui portaient l’arche, des chantres, et de Kenania, chef de musique parmi les chantres; et David avait sur lui un éphod de lin.
28 Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
Tout Israël fit monter l’arche de l’alliance de l’Éternel avec des cris de joie, au son des clairons, des trompettes et des cymbales, et en faisant retentir les luths et les harpes.
29 Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.
Comme l’arche de l’alliance de l’Éternel entrait dans la cité de David, Mical, fille de Saül, regardait par la fenêtre, et voyant le roi David sauter et danser, elle le méprisa dans son cœur.