< 1 Tarihi 15 >
1 Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
Et il fit pour lui des maisons dans la ville de David, et prépara un lieu pour l’arche de Dieu, et tendit une tente pour elle.
2 Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
Alors David dit: Il ne convient pas que l’arche de Dieu soit portée par personne excepté les Lévites; car l’Éternel les a choisis pour porter l’arche de Dieu et pour en faire le service à toujours.
3 Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
Et David assembla tout Israël à Jérusalem, pour faire monter l’arche de l’Éternel au lieu qu’il lui avait préparé.
4 Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
Et David assembla les fils d’Aaron et les Lévites:
5 Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
des fils de Kehath, Uriel, le chef, et ses frères, 120 [hommes];
6 daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
des fils de Merari, Asçaïa, le chef, et ses frères, 220;
7 daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
des fils de Guershom, Joël, le chef, et ses frères, 130;
8 daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
des fils d’Élitsaphan, Shemahia, le chef, et ses frères, 200;
9 daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
des fils de Hébron, Éliel, le chef, et ses frères, 80;
10 daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
des fils d’Uziel, Amminadab, le chef, et ses frères, 112.
11 Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
Et David appela Tsadok et Abiathar, les sacrificateurs, et les Lévites, Uriel, Asçaïa, et Joël, Shemahia, et Éliel, et Amminadab;
12 Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
et il leur dit: Vous êtes les chefs des pères des Lévites; sanctifiez-vous, vous et vos frères, et faites monter l’arche de l’Éternel, le Dieu d’Israël, au [lieu que] je lui ai préparé.
13 Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
Car, parce que vous ne l’avez pas [fait] la première fois, l’Éternel, notre Dieu, a fait une brèche parmi nous; car nous ne l’avons pas recherché conformément à l’ordonnance.
14 Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Et les sacrificateurs et les Lévites se sanctifièrent pour faire monter l’arche de l’Éternel, le Dieu d’Israël.
15 Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
Et les fils des Lévites portèrent l’arche de Dieu sur leurs épaules, avec les barres sur eux, comme Moïse l’avait commandé, selon la parole de l’Éternel.
16 Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
Et David dit aux chefs des Lévites d’établir leurs frères, les chantres, avec des instruments de musique, des luths, et des harpes, et des cymbales, qu’ils feraient retentir en élevant leur voix avec joie.
17 Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
Et les Lévites établirent Héman, fils de Joël; et, d’entre ses frères, Asaph, fils de Bérékia; et, d’entre les fils de Merari, leurs frères, Éthan, fils de Kushaïa;
18 Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
et avec eux leurs frères du second rang: Zacharie, Ben, et Jaaziel, et Shemiramoth, et Jekhiel, et Unni, Éliab, et Benaïa, et Maascéïa, et Matthithia, et Éliphelé, et Miknéïa, et Obed-Édom, et Jehiel, les portiers.
19 Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
Et les chantres, Héman, Asaph, et Éthan, avec des cymbales d’airain, pour les faire retentir;
20 Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
et Zacharie, et Aziel, et Shemiramoth, et Jekhiel, et Unni, et Éliab, et Maascéïa, et Benaïa, avec des luths, sur [le mode] d’Alamoth;
21 Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
et Matthithia, et Éliphelé, et Miknéïa, et Obed-Édom, et Jehiel, et Azazia, avec des harpes sur [le mode] de Sheminith, pour diriger le chant.
22 Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
Et Kenania, le chef des Lévites pour la musique, enseignait la musique; car il était intelligent.
23 Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
Et Bérékia et Elkana étaient portiers pour l’arche.
24 Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
Et Shebania, et Josaphat, et Nethaneël, et Amasçaï, et Zacharie, et Benaïa, et Éliézer, les sacrificateurs, sonnaient avec des trompettes devant l’arche de Dieu; et Obed-Édom et Jekhija étaient portiers pour l’arche.
25 Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
Et David, et les anciens d’Israël, et les chefs de milliers, allèrent pour faire monter l’arche de l’alliance de l’Éternel, de la maison d’Obed-Édom, avec joie:
26 Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
et il arriva que, quand Dieu aida les Lévites qui portaient l’arche de l’alliance de l’Éternel, ils sacrifièrent sept veaux et sept béliers.
27 To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
Et David était vêtu d’une robe de byssus, ainsi que tous les Lévites qui portaient l’arche, et les chantres, et Kenania, le chef de la musique des chantres; et David avait sur lui un éphod de lin.
28 Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
Et tout Israël faisait monter l’arche de l’alliance de l’Éternel avec des cris de joie, et au son du cor, et avec des trompettes et des cymbales, et en faisant retentir des luths et des harpes.
29 Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.
Et comme l’arche de l’alliance de l’Éternel arrivait à la ville de David, Mical, fille de Saül, regarda par la fenêtre, et elle vit le roi David sautant et jouant, et elle le méprisa dans son cœur.