< 1 Tarihi 15 >
1 Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
And he makes houses for himself in the City of David, and prepares a place for the Ark of God, and stretches out a tent for it.
2 Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
Then David said, “None [are] to carry the Ark of God, except the Levites, for YHWH has fixed on them to carry the Ark of God and to serve Him for all time.”
3 Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
And David assembles all Israel to Jerusalem, to bring up the Ark of YHWH to its place that he had prepared for it.
4 Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
And David gathers the sons of Aaron and the Levites—
5 Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
of sons of Kohath: Uriel the chief and one hundred and twenty of his brothers;
6 daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
of sons of Merari: Asaiah the chief and two hundred and twenty of his brothers;
7 daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
of sons of Gershom: Joel the chief and one hundred and thirty of his brothers;
8 daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
of sons of Elizaphan: Shemaiah the chief and two hundred of his brothers;
9 daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
of sons of Hebron: Eliel the chief and eighty of his brothers;
10 daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
of sons of Uzziel: Amminadab the chief and one hundred and twelve of his brothers.
11 Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
And David calls to Zadok and to Abiathar the priests, and to the Levites, to Uriel, Asaiah, and Joel, Shemaiah, and Eliel, and Amminadab,
12 Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
and says to them, “You [are] heads of the fathers of the Levites; sanctify yourselves, you and your brothers, and you have brought up the Ark of YHWH, God of Israel, to [the place] I have prepared for it;
13 Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
because you [did] not [do it] at the first, our God YHWH made a breach on us, because we did not seek Him according to the ordinance.”
14 Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And the priests and the Levites sanctify themselves to bring up the Ark of YHWH, God of Israel;
15 Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
and sons of the Levites carry the Ark of God, as Moses commanded, according to the word of YHWH, above them with poles on their shoulder.
16 Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
And David says to the heads of the Levites to appoint their brothers the singers, with instruments of song, psalteries, and harps, and cymbals, sounding, to lift up with the voice for joy.
17 Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
And the Levites appoint Heman son of Joel, and of his brothers, Asaph son of Berechiah, and of the sons of Merari their brothers, Ethan son of Kushaiah;
18 Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
and with them their brothers, the seconds [in rank]: Zechariah, Ben, and Jaaziel, and Shemiramoth, and Jehiel, and Unni, Eliab, and Benaiah, and Maaseiah, and Mattithiah, and Elipheleh, and Mikneiah; and Obed-Edom and Jeiel the gatekeepers;
19 Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
and the singers, Heman, Asaph, and Ethan, [are] to sound with cymbals of bronze;
20 Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
and Zechariah, and Aziel, and Shemiramoth, and Jeheil, and Unni, and Eliab, and Maaseiah, and Benaiah, with psalteries over the girls’ [voices],
21 Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
and Mattithiah, and Elipheleh, and Mikneiah, and Obed-Edom, and Jeiel, and Azaziah, to oversee with harps on the eighth.
22 Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
And Chenaniah, head of the Levites, [is] over the burden; he instructs about the burden, for he [is] intelligent.
23 Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
And Berechiah and Elkanah [are] gatekeepers for the Ark.
24 Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
And Shebaniah, and Joshaphat, and Nethaneel, and Amasai, and Zechariah, and Benaiah, and Eliezer the priests, are blowing with trumpets before the Ark of God; and Obed-Edom and Jehiah [are] gatekeepers for the Ark.
25 Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
And it is David, and [the] elderly of Israel, and the heads of the thousands, who are going to bring up the Ark of the Covenant of YHWH from the house of Obed-Edom with joy;
26 Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
and it comes to pass, in God’s helping the Levites carrying the Ark of the Covenant of YHWH, that they sacrifice seven bullocks and seven rams.
27 To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
And David is wrapped in an upper robe of fine linen, and all the Levites who are carrying the Ark, and the singers, and Chenaniah head of the burden of the singers; and an Ephod of linen [is] on David.
28 Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
And all of Israel is bringing up the Ark of the Covenant of YHWH with shouting, and with the sound of a horn, and with trumpets, and with cymbals, sounding with psalteries and harps,
29 Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.
and it comes to pass, the Ark of the Covenant of YHWH is entering into the City of David, and Michal daughter of Saul is looking through the window, and sees King David dancing and playing, and despises him in her heart.