< 1 Tarihi 14 >

1 To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
Kongen i Tyrus Hiram skikket sendemenn til David med sedertre, og han sendte stenhuggere og tømmermenn til å bygge et hus for ham.
2 Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
Og David forstod at Herren hadde stadfestet hans kongedømme over Israel; for hans rike var blitt hevet høit for hans folk Israels skyld.
3 A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
David tok ennu flere hustruer i Jerusalem, og han fikk ennu flere sønner og døtre.
4 Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
Dette er navnene på de sønner han fikk i Jerusalem: Sammua og Sobab, Natan og Salomo
5 Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
og Jibhar og Elisua og Elpelet
6 Noga, Nefeg, Yafiya,
og Nogah og Nefeg og Jafia
7 Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
og Elisama og Be'eljada og Elifelet.
8 Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
Da filistrene hørte at David var salvet til konge over hele Israel, drog alle filistrene ut for å søke efter David; og da David hørte det, drog han ut imot dem.
9 To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
Og filistrene kom og spredte sig utover i Refa'im-dalen.
10 sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
Da spurte David Gud: Skal jeg dra ut mot filistrene, og vil du gi dem i min hånd? Og Herren svarte: Dra ut! Så vil jeg gi dem i din hånd.
11 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
Så drog de op til Ba'al-Perasim, og der slo David dem, og David sa: Gud har brutt igjennem mine fiender ved min hånd, som vannene bryter igjennem. Derfor blev dette sted kalt Ba'al-Perasim.
12 Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
Der lot de efter sig sine guder, og David bød at de skulde brennes op med ild.
13 Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
Men filistrene kom igjen og spredte sig utover i dalen.
14 sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
Og David spurte atter Gud, og Gud sa til ham: Du skal ikke dra op efter dem; vend dig fra dem og ta en omvei, så du kommer over dem midt for bakatrærne,
15 Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
og når du hører lyden av skritt i bakatrærnes topper, da skal du dra ut i striden; for Gud har draget ut foran dig for å slå filistrenes hær.
16 Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
David gjorde som Gud hadde befalt ham, og de slo filistrenes hær og forfulgte dem fra Gibeon og like til Geser.
17 Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.
og Davids navn kom ut i alle landene, og Herren lot frykt for ham komme over alle folkene.

< 1 Tarihi 14 >