< 1 Tarihi 14 >

1 To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
Et Hiram Roi de Tyr envoya des messagers à David, et du bois de cèdre, et des maçons, et des charpentiers, pour lui bâtir une maison.
2 Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
Alors David connut que l'Eternel l'avait affermi Roi sur Israël, parce que son règne avait été fort élevé, pour l'amour de son peuple d'Israël.
3 A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
Et David prit encore des femmes à Jérusalem, et il engendra encore des fils et des filles.
4 Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
Et ce sont ici les noms des enfants qu'il eut à Jérusalem, Sammuah, Sobab, Nathan, Salomon,
5 Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
Jibhar, Elisuah, Elpélet,
6 Noga, Nefeg, Yafiya,
Nogah, Népheg, Japhiah,
7 Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
Elisamah, Béël-jadah, et Eliphelet.
8 Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
Or quand les Philistins eurent su que David avait été oint pour Roi sur tout Israël, ils montèrent tous pour chercher David; et David l'ayant appris, sortit au devant d'eux.
9 To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
Et les Philistins vinrent, et se répandirent dans la vallée des Réphaïms.
10 sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
Et David consulta Dieu, en disant: Monterai-je contre les Philistins, et les livreras-tu entre mes mains? Et l'Eternel lui répondit: Monte, et je les livrerai entre tes mains.
11 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
Alors ils montèrent à Bahal-pératsim, et David les battit là; et il dit: Dieu a fait écouler mes ennemis par ma main, comme un débordement d'eaux; c'est pourquoi on nomma ce lieu-là Bahal-pératsim.
12 Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
Et ils laissèrent là leurs dieux; et David commanda qu'on les brûlât au feu.
13 Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
Et les Philistins se répandirent encore une autre fois dans cette même vallée.
14 sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
Et David consulta encore Dieu; et Dieu lui répondit: Tu ne monteras point vers eux, mais tu tournoieras autour d'eux, et tu iras contr'eux vis-à-vis des mûriers.
15 Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
Et sitôt que tu auras entendu aux sommets des mûriers un bruit [comme de gens] qui marchent, tu sortiras alors au combat; car Dieu sera sorti devant toi pour frapper le camp des Philistins.
16 Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
David donc fit selon ce que Dieu lui avait commandé; et on frappa le camp des Philistins, depuis Gabaon jusqu'à Guézer.
17 Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.
Ainsi la renommée de David se répandit par tous ces pays-là; et l'Eternel remplit de frayeur toutes ces nations-là, [au seul nom de David].

< 1 Tarihi 14 >