< 1 Tarihi 14 >
1 To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
One day Hiram, the king of Tyre [city], sent some messengers to David [to talk about making an agreement between their countries]. Then Hiram sent cedar logs, bricklayers, and carpenters to build a palace for David.
2 Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
[When that happened, ] David knew that Yahweh had truly caused him to be the king of Israel, and that he had caused his kingdom to be greatly respected. Yahweh did this because [he loved] his Israeli people.
3 A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
David married more women in Jerusalem, and [those women] gave birth to more sons and daughters for him.
4 Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
The names of the children that were born to him there in Jerusalem are Shammua, Shobab, Nathan, Solomon,
5 Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
Ibhar, Elishua, Elpelet,
7 Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
Elishama, Beeliada, and Eliphelet.
8 Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
When the army of Philistia heard that David has been appointed to be king of all of Israel, they came to capture him. But David heard that they were coming, so he [and his soldiers] marched out to fight against them.
9 To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
The army of Philistia had attacked the people in the Rephaim Valley [southwest of Jerusalem] and had robbed them.
10 sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
David asked God, “Should [my men and] I go and attack the army of Philistia? [If we go, ] will you enable us to defeat [IDM] them?” Yahweh replied, “Yes, go, and I will enable you to defeat [IDM] them.”
11 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
So David and his men went up to a town where the soldiers of Philistia were staying and defeated them. Then David said, “God has enabled me [and my soldiers] to overwhelm my enemies like [MET] a flood.” So they named that place {That place is called} ‘Baal-Perazim’ [which means ‘Yahweh breaks through’].
12 Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
[As the soldiers of Philistia fled], they left their idols there. So David commanded his soldiers to burn those idols.
13 Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
But soon the army of Philistia attacked the people in that valley again.
14 sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
So again David prayed to God [to ask him what he should do], and God replied, saying “Do not attack the army of Philistia from the front. Instead, go around them, and attack them [from the rear] in front of the balsam trees.
15 Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
When you hear something in the tops of the balsam trees that sounds like [soldiers] marching, attack them. I, God, will have gone ahead of you to enable you to defeat the army of Philistia.”
16 Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
So David did what God commanded him to do, and he and his army defeated the army of Philistia, all the way from Gibeon [city in the east] to Gezer [city in the west].
17 Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.
So David became famous in all the nearby countries, and Yahweh caused [the leaders of] all the [nearby] nations to be afraid of him.