< 1 Tarihi 14 >

1 To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
And Huram king of Tyre sends messengers to David, and cedar-wood, and craftsmen of walls, and craftsmen of wood, to build a house for him.
2 Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
And David knows that YHWH has established him for king over Israel, because of the lifting up on high of his kingdom, for the sake of His people Israel.
3 A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
And David takes wives again in Jerusalem, and David begets sons and daughters again;
4 Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
and these [are] the names of the children whom he has in Jerusalem: Shammua, and Shobab, Nathan, and Solomon,
5 Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
and Ibhar, and Elishua, and Elpalet,
6 Noga, Nefeg, Yafiya,
and Nogah, and Nepheg, and Japhia,
7 Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
and Elishama, and Beeliada, and Eliphalet.
8 Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
And the Philistines hear that David has been anointed for king over all Israel, and all the Philistines go up to seek David, and David hears, and goes out before them.
9 To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
And the Philistines have come, and rush into the Valley of Rephaim,
10 sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
and David asks of God, saying, “Do I go up against the Philistines—and have You given them into my hand?” And YHWH says to him, “Go up, and I have given them into your hand.”
11 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
And they go up into Ba‘al-Perazim, and David strikes them there, and David says, “God has broken up my enemies by my hand, like the breaking up of waters”; therefore they have called the name of that place Ba‘al-Perazim.
12 Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
And they leave their gods there, and David commands, and they are burned with fire.
13 Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
And the Philistines add again, and rush into the valley,
14 sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
and David asks again of God, and God says to him, “Do not go up after them, turn around from them, and you have come to them from the front [[or in front]] of the mulberries;
15 Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
and it comes to pass, when you hear the sound of the stepping at the heads of the mulberries, then you go out into battle, for God has gone out before you to strike the camp of the Philistines.”
16 Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
And David does as God commanded him, and they strike the camp of the Philistines from Gibeon even to Gazer;
17 Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.
and the name of David goes out into all the lands, and YHWH has put his fear on all the nations.

< 1 Tarihi 14 >