< 1 Tarihi 14 >
1 To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
Then Hiram, king of Tyre, sent messengers to David along with cedar timber, stonemasons, and carpenters to build him a palace.
2 Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
In this way David realized that the Lord had placed him on the throne as king of Israel and had blessed by supporting his kingdom for the sake of the Lord's people Israel.
3 A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
David married more wives in Jerusalem, and had more sons and daughters.
4 Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
This is a list of the names of the children he had in Jerusalem: Shammua, Shobab, Nathan, Solomon,
5 Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
Ibhar, Elishua, Elpelet,
7 Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
Elishama, Beeliada, and Eliphelet.
8 Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
When the Philistines heard that David had been anointed king over all of Israel, they gathered their whole army to go after him. But David heard they were coming and went out to confront them.
9 To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
The Philistines arrived and raided the valley of Rephaim.
10 sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
David consulted God, asking “Shall I go and attack the Philistines? Will you make me victorious over them?” “Go ahead,” the Lord told him, “I will make you victorious over them.”
11 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
So David attacked and defeated them there at Baal-perazim. “God used me to defeat my enemies like a torrent of water that bursts out,” he declared. That's why the place was named Baal-perazim.
12 Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
The Philistines had left their gods behind, so David gave orders that they should be burned.
13 Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
However, the Philistines returned and made another raid on the valley.
14 sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
David consulted God again. “Don't make a frontal attack,” God told him. “Instead go around behind them and attack them in front of the balsam trees.
15 Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
As soon as you hear the sound of marching in the tops of the balsam trees, go and attack for the Lord has gone before you to strike down the Philistine army.”
16 Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
So David did what God told him, striking down the Philistine army all the way from Gibeon to Gezer.
17 Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.
As a result David's reputation was spread everywhere, and the Lord made all the nations afraid of David.