< 1 Tarihi 14 >

1 To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
And Chiram king of Tyre sent messengers to David, and cedar timbers, and masons, and carpenters, to build a house for him.
2 Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
And David knew that the Lord [had] designed him to be king over Israel; because his kingdom was highly exalted, on account of his people Israel.
3 A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
And David took more wives in Jerusalem: and there were born to David more sons and daughters.
4 Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
And these [are] the names of those that were born, who were [born] to him in Jerusalem; Samaa, Sobab, Nathan, and Solomon,
5 Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
and Baar, and Elisa, and Eliphaleth,
6 Noga, Nefeg, Yafiya,
and Nageth, and Naphath, and Japhie,
7 Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
and Elisamae, and Eliade, and Eliphala.
8 Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
And the Philistines heard that David was anointed king over all Israel: and all the Philistines went up to seek David; and David heard [it], and went out to meet them.
9 To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
And the Philistines came and assembled together in the giants' valley.
10 sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
And David enquired of God, saying, Shall I go up against the Philistines? and wilt thou deliver them into my hand? And the Lord said to him, Go up, and I will deliver them into thy hands.
11 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
And he went up to Baal Pharasin, and David smote them there; and David said, God has broken through enemies by my hand like a breach of water: therefore he called the name of that place, the Breach of Pharasin.
12 Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
And the Philistines left their gods there; and David gave orders to burn them with fire.
13 Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
And the Philistines once more assembled themselves in the giants' valley.
14 sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
And David enquired of God again; and God said to him, Thou shalt not go after them; turn away from them, and thou shalt come upon them near the pear trees.
15 Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
And it shall be, when thou shalt hear the sound of their tumult in the tops of the pear trees, then thou shalt go into the battle: for God has gone out before thee to smite the army of the Philistines.
16 Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
And he did as God commanded him: and he smote the army of the Philistines from Gabaon to Gazera.
17 Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.
And the name of David was [famous] in all the land; and the Lord put the terror of him on all the nations.

< 1 Tarihi 14 >