< 1 Tarihi 14 >
1 To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
Kong Hiram af Tyrus sendte Sendebud til David med Cedertræer og tillige Murere og Tømmermænd for at bygge ham et Hus.
2 Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
Da skønnede David, at HERREN havde sikret hans Kongemagt over Israel og højnet hans Kongedømme for sit Folk Israels Skyld.
3 A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
David tog i Jerusalem endnu flere Hustruer og avlede flere Sønner og Døtre.
4 Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
Navnene på de Børn, han fik i Jerusalem, er følgende: Sjammua, Sjobab, Natan, Salomo,
5 Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
Jibhar, Elisjua, Elpelet,
7 Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
Elisjama, Be'eljada og Elifelet.
8 Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
Men da Fiilisterne hørte, at David var salvet til Konge over hele Israel, rykkede de alle ud for at søge efter ham. Ved Efterretningen herom drog David ud for at møde dem,
9 To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
medens Filisterne kom og bredte sig i Refaimdalen.
10 sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
David rådspurgte da Gud: "Skal jeg drage op mod Filisterne? Vil du give dem i min Hånd?" Og HERREN svarede ham: "Drag op, thi jeg vil give dem i din Hånd!"
11 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
Så drog de op til Ba'al-Perazim, og der slog han dem. Da sagde David: "Gud har brudt igennem mine Fjender ved min Hånd, som Vand bryder igennem!" Derfor kalder man Stedet Ba'al-Perazim.
12 Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
Og de lod deres Guder i Stikken der, og David bød, at de skulde opbrændes.
13 Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
Men Filisterne bredte sig på ny i Dalen.
14 sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
Da David atter rådspurgte Gud, svarede han: "Drag ikke efter dem, men omgå dem og fald dem i Ryggen ud for Bakabuskene.
15 Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
Når du da hører Lyden af Skridt i Bakabuskenes Toppe, skal du drage i Kamp, thi så er Gud draget ud foran dig for at slå Filisternes Hær."
16 Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
David gjorde, som Gud bød, og de slog Filisternes Hær fra Gibeon til hen imod Gezer.
17 Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.
Og Davids Ry bredte sig i alle Lande, idet HERREN Iod Frygt for ham komme over alle Hedningefolkene.