< 1 Tarihi 13 >

1 Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
Davut binbaşılara, yüzbaşılara ve subaylarına danıştı.
2 Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
Sonra bütün İsrail topluluğuna şöyle seslendi: “Eğer onaylarsanız ve Tanrımız RAB'bin isteğiyse, İsrail ülkesinin her yanına yayılmış öbür soydaşlarımıza ve onlarla birlikte kendi kentlerinde ve otlaklarında yaşayan kâhinlerle Levililer'e haberciler gönderelim. Onlar da gelip bize katılsınlar.
3 Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
Tanrımız'ın Sandığı'nı geri getirelim. Çünkü Saul'un krallığı döneminde ona gereken önemi vermedik.”
4 Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
Topluluk bu öneriyi benimseyerek sandığı geri getirmeye karar verdi.
5 Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
Davut Tanrı'nın Antlaşma Sandığı'nı Kiryat-Yearim'den geri getirmek için Mısır'daki Şihor Irmağı'ndan Levo-Hamat'a kadar bütün İsrailliler'i topladı.
6 Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
Böylece Davut'la İsrailliler Keruvlar arasında taht kuran RAB Tanrı'nın adıyla anılan Tanrı'nın Antlaşma Sandığı'nı getirmek için Yahuda'daki Baala Kenti'ne –Kiryat-Yearim'e– gittiler.
7 Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
Tanrı'nın Sandığı'nı Avinadav'ın evinden alıp yeni bir arabaya koydular. Arabayı Uzza'yla Ahyo sürüyordu.
8 Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
Bu arada Davut'la bütün İsrail halkı da Tanrı'nın önünde lir, çenk, tef, zil ve borazanlar eşliğinde ezgiler okuyarak, var güçleriyle bu olayı kutluyorlardı.
9 Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
Kidon'un harman yerine vardıklarında öküzler tökezledi. Bu nedenle Uzza elini uzatıp sandığı tuttu.
10 Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
RAB sandığa elini uzatan Uzza'ya öfkelenerek onu yere çaldı. Uzza orada, Tanrı'nın önünde öldü.
11 Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
Davut, RAB'bin Uzza'yı cezalandırmasına öfkelendi. O günden bu yana oraya Peres-Uzza denilir.
12 Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
Davut o gün Tanrı'dan korkarak, “Tanrı'nın Sandığı'nı nasıl yanıma getirsem?” diye düşündü.
13 Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
Sandığı yanına, Davut Kenti'ne götüreceğine Gatlı Ovet-Edom'un evine götürdü.
14 Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.
Tanrı'nın Sandığı Gatlı Ovet-Edom'un evinde üç ay kaldı. RAB Ovet-Edom'un ailesini ve ona ait her şeyi kutsadı.

< 1 Tarihi 13 >