< 1 Tarihi 13 >

1 Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
KUKA ae la o Davida me na luna tausani a me na luna haneri, a me na luna a pau.
2 Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
Olelo mai o Davida i ke anaina kanaka a pau o ka Iseraela, Ina he maikai keia ia oukou, a ina na Iehova mai o ko kakou Akua ia mea, e hoouna aku kakou a i na hoahanau o kakou ma na wahi a pau, e waiho ana ma na aina a pau o ka Iseraela, a me lakou pu i na kahuna a me ka Levi iloko o ko lakou mau kulanakauhale a me na kula, e akoakoa mai ai lakou io kakou nei:
3 Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
A e lawe mai kakou i ka pahu o ko kakou Akua io kakou nei: no ka mea, aole kakou i ninau aku ma ia mea i na la o Saula.
4 Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
Olelo aku la ke anaina kanaka a pau, e hana lakou pela: no ka mea, he maikai ia mea imua o na kanaka a pau.
5 Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
Pela i houluulu ai o Davida i ka Iseraela a pau i kahi hookahi, mai Sihora o Aigupita a hiki aku i ke komo ana aku i Hemata, e lawe i ka pahu o ko Akua mai Kiriataiearima mai.
6 Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
Pii aku la o Davida, a me ka Iseraela a pau a Baala, oia o Kiriataiearima, no ka Iuda, mailaila mai e lawe i ka pahu o ke Akua o Iehova, e noho ana mawaena o na keruba, kahi i heaia'i kona inoa.
7 Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
Hooholo ae la lakou i ka pahu o ke Akua maluna o ko kaa hou, mai ka hale mai o Abinadaba; a kai aku la o Uza laua o Ahio i ke kaa.
8 Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
Hookani aku la o Davida a me ka Iseraela a pau imua o ke Akua me ka ikaika a pau, i na mele, me na lira, na pesaleteria, na timeberela, na kimebala, a me na pukani.
9 Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
A hiki aku lakou i kahi hehi-palaoa no Kidona, hoo aku la o Uza i kona lima a hoopaa i ka pahu: no ka mea, okupe iho la na bipikauo.
10 Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
Ua hoaia ka inaina o Iehova ia Uza, a hahau mai la oia ia ia, no ka mea, ua lalau kona lima i ka pahu; a make iho la ia ilaila imua o ko Akua.
11 Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
Ukiuki iho la o Davida i ko Iehova hahau ana ia Uza; nolaila ua kapaia ka inoa o ia wahi o Perezuza a hiki i keia la.
12 Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
Makau iho la o Davida i ke Akua ia la, i iho la, Pehea la ka'u e lawe mai ai i ka pahu o ke Akua io'u nei?
13 Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
Nolaila, aole i lawe mai o Davida i ka pahu berita io na la i ke kulanakauhale o Davida: aka, lawe ae la oia ia mea maloko o ka hale o Obededoma ka Gata.
14 Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.
A waiho iho la ka pahu o ke Akua me ka ohana a Obededoma iloko o kona hale i na malama ekolu. A hoopomaikai o Iehova i ko ka hale o Obededoma, a me kona mau mea a pau.

< 1 Tarihi 13 >