< 1 Tarihi 13 >

1 Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
Or David tint conseil avec les chefs de milliers et de centaines, avec tous les conducteurs du peuple.
2 Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
Et David dit à toute l'assemblée d'Israël: S'il vous semble bon, et que cela vienne de l'Éternel, notre Dieu, envoyons de tous côtés vers nos autres frères qui restent dans toutes les contrées d'Israël, et aussi vers les sacrificateurs et les Lévites, dans leurs villes à banlieues, afin qu'ils se réunissent à nous,
3 Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
Et ramenons auprès de nous l'arche de notre Dieu; car nous ne l'avons point recherchée du temps de Saül.
4 Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
Et toute l'assemblée décida de faire ainsi, car la chose fut approuvée par tout le peuple.
5 Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
David assembla donc tout Israël, depuis le Shichor d'Égypte, jusqu'à l'entrée de Hamath, pour ramener l'arche de Dieu de Kirjath-Jearim.
6 Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
Et David monta avec tout Israël à Baala, à Kirjath-Jearim qui est à Juda, pour faire monter de là l'arche de Dieu, l'Éternel, qui habite entre les chérubins, et dont le nom y est invoqué.
7 Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
Ils mirent donc l'arche de Dieu sur un chariot neuf, et l'emmenèrent de la maison d'Abinadab; et Uzza et Achjo conduisaient le chariot.
8 Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
Et David et tout Israël dansaient devant Dieu de toute leur force, en chantant, et en jouant des harpes, des lyres, des tambourins, des cymbales et des trompettes.
9 Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
Quand ils furent venus jusqu'à l'aire de Kidon, Uzza étendit la main pour retenir l'arche, parce que les bœufs regimbaient.
10 Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
Mais la colère de l'Éternel s'enflamma contre Uzza, et il le frappa, parce qu'il avait étendu la main sur l'arche; et il mourut là devant Dieu.
11 Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
Et David fut affligé de ce que l'Éternel avait fait une brèche, en la personne d'Uzza; et on a appelé jusqu'à ce jour ce lieu Pérets-Uzza (Brèche d'Uzza).
12 Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
David eut peur de Dieu en ce jour-là, et il dit: Comment ferais-je entrer chez moi l'arche de Dieu?
13 Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
Aussi David ne retira pas l'arche chez lui, dans la cité de David; mais il la fit conduire dans la maison d'Obed-Édom, le Guitthien.
14 Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.
L'arche de Dieu resta trois mois avec la famille d'Obed-Édom, dans sa maison. Et l'Éternel bénit la maison d'Obed-Édom et tout ce qui était à lui.

< 1 Tarihi 13 >