< 1 Tarihi 13 >

1 Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
Or David demanda conseil aux chefs de milliers, et de centaines, et à tous les conducteurs [du peuple].
2 Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
Et il dit à toute l'assemblée d'Israël: Si vous l'approuvez, et que [cela vienne] de l'Eternel notre Dieu, envoyons partout vers nos autres frères qui sont dans toutes les contrées d'Israël, et avec lesquels sont les Sacrificateurs et les Lévites, dans leurs villes et dans leurs faubourgs, afin qu'ils s'assemblent vers nous;
3 Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
Et que nous ramenions auprès de nous l'Arche de notre Dieu; car nous ne l'avons pas recherchée aux jours de Saül.
4 Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
Et toute l'assemblée répondit qu'on le fît ainsi; car la chose avait été trouvée bonne par tout le peuple.
5 Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
David donc assembla tout Israël, depuis Sihor, [le torrent] d'Egypte, jusqu'à l'entrée [du pays] de Hamath, pour ramener de Kirjath-jéharim l'Arche de Dieu.
6 Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
Et David monta avec tout Israël [vers] Bahala à Kirjath-jéharim, qui appartient à Juda, pour faire amener de là l'Arche de Dieu l'Eternel, qui habite entre les chérubins, le nom duquel est invoqué.
7 Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
Et ils mirent l'Arche de Dieu sur un chariot neuf, [et l'emmenèrent] de la maison d'Abinadab; et Huza et Ahio conduisaient le chariot.
8 Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
Et David et tout Israël jouaient en la présence de Dieu de toute leur force, des cantiques, sur des violons, des musettes, des tambours, des cymbales, et des trompettes.
9 Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
Et quand ils furent arrivés à l'aire de Kidon, Huza étendit sa main pour retenir l'Arche, parce que les bœufs avaient glissé.
10 Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
Et la colère de l'Eternel s'enflamma contre Huza, qui le frappa, parce qu'il avait étendu sa main contre l'Arche; et il mourut en la présence de Dieu.
11 Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
Et David fut affligé de ce que l'Eternel avait fait une brèche en la personne de Huza; et on a appelé jusqu'à aujourd'hui le nom de ce lieu-là, Pérets-Huza.
12 Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
Et David eut peur de Dieu en ce jour-là, et il dit: Comment ferais-je entrer chez moi l'Arche de Dieu?
13 Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
C'est pourquoi David ne la retira point chez lui, dans la Cité de David; mais il la fit détourner dans la maison d'Hobed-Edom Guittien.
14 Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.
Et l'Arche de Dieu demeura trois mois avec la famille d'Hobed-Edom, dans sa maison; et l'Eternel bénit la maison d'Hobed-Edom, et tout ce qui lui appartenait.

< 1 Tarihi 13 >