< 1 Tarihi 13 >

1 Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
David consulta les chefs de milliers et de centaines, et tous les chefs.
2 Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
David dit à toute l'assemblée d'Israël: « Si cela vous paraît bon et si c'est l'avis de l'Éternel, notre Dieu, envoyons partout des messages à nos frères qui sont restés dans tout le pays d'Israël, avec lesquels les prêtres et les lévites sont dans leurs villes qui ont des pâturages, afin qu'ils se rassemblent auprès de nous.
3 Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
Et aussi, ramenons chez nous l'arche de notre Dieu, car nous ne l'avons pas cherchée du temps de Saül. »
4 Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
Toute l'assemblée répondit qu'elle le ferait, car la chose était bonne aux yeux de tout le peuple.
5 Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
Et David rassembla tout Israël, depuis le fleuve Shihor en Égypte jusqu'à l'entrée de Hamath, pour faire venir l'arche de Dieu de Kiriath Jearim.
6 Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
David monta avec tout Israël à Baala, c'est-à-dire à Kiriath Jearim, qui appartenait à Juda, pour faire monter de là l'arche de Dieu Yahvé, qui est assise au-dessus des chérubins et qui porte le nom de Yahvé.
7 Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
Ils portèrent l'arche de Dieu sur un char neuf, et l'amenèrent de la maison d'Abinadab; Uzza et Ahio conduisaient le char.
8 Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
David et tout Israël jouèrent devant Dieu de toute leur force, avec des chants, avec des harpes, avec des instruments à cordes, avec des tambourins, avec des cymbales et avec des trompettes.
9 Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
Lorsqu'ils arrivèrent à l'aire de Chidon, Uzza étendit la main pour tenir l'arche, car les bœufs trébuchaient.
10 Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
La colère de Yahvé s'enflamma contre Uzza, et il le frappa parce qu'il avait mis la main sur l'arche; et il mourut là, devant Dieu.
11 Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
David fut mécontent, car Yahvé s'était déchaîné contre Uzza. Il appela ce lieu Perez Uzza, jusqu'à ce jour.
12 Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
Ce jour-là, David eut peur de Dieu et dit: « Comment pourrais-je ramener chez moi l'arche de Dieu? »
13 Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
David ne transporta donc pas l'arche avec lui dans la ville de David, mais il la porta à l'écart, dans la maison d'Obed-Edom, le Gittien.
14 Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.
L'arche de Dieu resta trois mois dans la maison d'Obed-Edom, et Yahvé bénit la maison d'Obed-Edom et tout ce qui lui appartenait.

< 1 Tarihi 13 >