< 1 Tarihi 13 >

1 Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
And David consulted with the captains of thousands and of hundreds, even with every leader.
2 Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
And David said unto, all the assembly of Israel, If it seem good unto you, and if it be of the LORD our God, let us send abroad every where unto our brethren that are left in all the land of Israel, with whom the priests and Levites are in their cities that have suburbs, that they may gather themselves unto us:
3 Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
and let us bring again the ark of our God to us: for we sought not unto it in the days of Saul.
4 Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
And all the assembly said that they would do so: for the thing was right in the eyes of all the people.
5 Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
So David assembled all Israel together, from Shihor [the brook] of Egypt even unto the entering in of Hamath; to bring the ark of God from Kiriath-jearim.
6 Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
And David went up, and all Israel, to Baalah, [that is], to Kiriath-jearim, which belonged to Judah, to bring up from thence the ark of God, the LORD that sitteth upon the cherubim, which is called by the Name.
7 Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
And they carried the ark of God upon a new cart, [and brought it] out of the house of Abinadab: and Uzza and Ahio drave the cart.
8 Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
And David and all Israel played before God with all their might: even with songs, and with harps, and with psalteries, and with timbrels, and with cymbals, and with trumpets.
9 Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
And when they came unto the threshing-floor of Chidon, Uzza put forth his hand to hold the ark; for the oxen stumbled.
10 Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
And the anger of the LORD was kindled against Uzza, and he smote him, because he put forth his hand to the ark: and there he died before God.
11 Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
And David was displeased, because the LORD had broken forth upon Uzza: and he called that place Perez-uzza, unto this day.
12 Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
And David was afraid of God that day, saying, How shall I bring the ark of God home to me?
13 Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
So David removed not the ark unto him into the city of David, but carried it aside into the house of Obed-edom the Gittite.
14 Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.
And the ark of God remained with the family of Obed-edom in his house three months: and the LORD blessed the house of Obed-edom, and all that he had.

< 1 Tarihi 13 >