< 1 Tarihi 13 >

1 Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
And David consulted with the officers of the thousands and hundreds, and with every leader.
2 Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
And David said unto all the congregation of Israel, if it seem good unto you, and if it be of the Lord our God, let us send widely about unto our brethren who are left in all the lands of Israel, and with them unto the priests and Levites who are in their cities and open districts, that they may gather themselves together unto us.
3 Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
And let us bring round the ark of our God to us; for we have inquired not at it in the days of Saul.
4 Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
And all the congregation said that this should be done; for the king was right in the eyes of all the people.
5 Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
So David assembled all Israel together, from Shichor of Egypt even unto the entrance of Chemath, to bring the ark of God from Kiryath-ye'arim.
6 Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
And David went up, with all Israel, to Ba'alah, [that is] to Kiryath-ye'arim, which belonged to Judah, to bring up thence the ark of God the Lord, that dwelleth between the cherubim, whose name is called [on it].
7 Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
And they conveyed the ark of God in a new wagon out of the house of Abinadab: and 'Uzza and Achyo guided the wagon.
8 Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
And David and all Israel played before God with all their might, and with singing, and on harps, and on psalteries, and on tambourines, and with cymbals, and with trumpets.
9 Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
And when they came as far as the threshing-floor of Kidon, 'Uzza put forth his hand to take hold of the ark; for the oxen shook it.
10 Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
And the anger of the Lord was kindled against 'Uzza, and he smote him, because he had put forth his hand toward the ark: and he died there before God.
11 Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
And it was grievious to David, because the Lord had suddenly taken away 'Uzza; and he called that place Perez-'uzza [[Breach of 'Uzza]] until this day.
12 Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
And David was afraid of God that day, saying, How shall I bring home to me the ark of God?
13 Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
So David removed not the ark unto himself into the city of David, but had it carried round into the house of 'Obed-edom the Gittite.
14 Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.
And the ark of God remained in the house of 'Obed-edom, in his house, three months. And the Lord blessed the house of 'Obed-edom, and all that belonged to him.

< 1 Tarihi 13 >