< 1 Tarihi 12 >

1 Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
Also these camen to Dauid in Sichelech, whanne he fledde yit fro Saul, the sone of Cys; whiche weren strongeste men and noble fiyterys,
2 suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
beendynge bouwe, and castynge stoonys with slyngis with euer either hond, and dressynge arowis; of the britheren of Saul of Beniamyn,
3 Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
the prince Achieser, and Joas, the sones of Samaa of Gabaath, and Jazachel, and Phallech, the sones of Azmod, and Barachie, and Jehu of Anathot;
4 da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
also Samay of Gabaon was the strongeste among thretti and aboue thretti; Jeremy, and Jezihel, and Johannan, and Zebadga Zerothites,
5 Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
Elusay, and Jerymoth, and Baalia, and Samaria, and Saphia Araphites,
6 Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
Elchana, and Jesia, and Azrahel, and Jezer, and Jesbaam of Taremy,
7 da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
and Joelam, and Sabadia, the sones of Jeroam of Jedor.
8 Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
But also of Gaddi strongeste men, and beste fiyteris, holdynge scheld and spere, fledden ouer to Dauid, whanne he was hid in deseert; the faces of hem as the face of a lioun, and thei weren swift as capretis in hillis.
9 Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
Ozer was the prince, Obdias the secounde, Eliab the thridde,
10 Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
Masmana the fourthe, Jeremye the fyuethe,
11 Attai na shida, Eliyel na bakwai,
Becchi the sixte, Heliel the seuenthe,
12 Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
Johannan the eiythe, Helzedad the nynthe,
13 Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
Jeremye the tenthe, Bachana the euleuenthe;
14 Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
these of the sones of Gad weren princes of the oost; the laste was souereyn ouer an hundrid knyytis, and the moost was souereyn ouer a thousynde.
15 Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
These it ben that passiden ouer Jordan in the firste monethe, whanne it was wont to flowe ouer hise brynkis; and thei dryueden awei alle men that dwelliden in the valeis at the eest coost and west coost.
16 Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
Sotheli also men of Beniamyn and of Juda camen to the stronge hoold, whereyn Dauid dwellide.
17 Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
And Dauid yede out ayens hem, and seide, If ye `ben comyn pesible to me, for to helpe me, myn herte be ioyned to you; forsothe if ye setten aspies to me for myn aduersaries, sithen Y haue not wickidnesse in the hondis, God of our fadris se and deme.
18 Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
Forsothe the spirit clothide Amasay, the prynce among thritti, and he seide, A! Dauid, we ben thin, and thou, sone of Ysai, we schulen be with thee; pees, pees to thee, and pees to thin helperis, for thi Lord God helpith thee. Therfor Dauid resseyuede hem, and made princes of the cumpeny.
19 Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
Forsothe men of Manasses fledden ouer to Dauid, whanne he cam with Filisteis to fiyte ayens Saul, and he fauyte not with hem, for after that the princes of Filisteis hadden take counsel, thei senten hym ayen, and seiden, With perel of oure heed he schal turne ayen to Saul his lord.
20 Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
Therfor whanne Dauid turnede ayen in to Sichelech, men of Manasses fledden ouer to hym, Eduas, and Jozabad, Jedihel, and Mychael, and Naas, and Jozabath, and Helyu, and Salathi, princes of knyytis in Manasses.
21 Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
These men yauen help to Dauid ayens theues; for alle weren strongeste men, and thei weren maad prynces in the oost.
22 Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
But also bi ech dai men camen to Dauid, for to helpe hym, til that the noumbre was maad greet as the oost of God.
23 Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
Also this is the noumbre of princes of the oost that camen to Dauid, whanne he was in Ebron, that thei schulden translate the rewme of Saul to hym, bi the word of the Lord; the sones of Juda,
24 Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
berynge scheeld and spere, sixe thousynde and eiyte hundrid, redi to batel;
25 mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
of the sones of Simeon, seuene thousinde and an hundrid, of strongeste men to fiyte;
26 mutanen Lawi, su 4,600,
of the sones of Leuy, foure thousynde and sixe hundrid;
27 haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
also Joiada, prince of the generacioun of Aaron, and thre thousynd and seuene hundrid with hym;
28 da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
also Sadoch, a child of noble wit, and the hows of his fadir, twei and twenti princes;
29 mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
forsothe of the sones of Beniamyn, britheren of Saul, thre thousynde; for a greet part of hem suede yit the hows of Saul;
30 mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
forsothe of the sones of Effraym, twenti thousynde and eiyte hundrid, strongeste men in bodili myyt, men named in her meynees;
31 mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
and of the half part of the lynage of Manasses, eiytene thousynde; alle camen bi her names, to make Dauid kyng;
32 mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
also of the sones of Ysacar, two hundrid princes, lernd men, that knewen ech tyme to comaunde what the puple of Israel ouyt to do; sotheli al the residue lynage suede the counseils of hem;
33 mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
forsothe of Zabulon camen fifti thousynde in to helpe, not in double herte, which yeden out to batel, and stoden in the scheltrun, and weren maad redi with armuris of batel;
34 mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
and of Neptalym a thousynde prynces, and with hem camen seuene and thritti thousynde men, arayed with scheeld and speere;
35 mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
also of Dan, eiyte and twenti thousynde and sixe hundrid men, maad redi to batel;
36 mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
and of Aser fourti thousynde men, goynge out to batel, and stirynge to batel in the scheltrun.
37 kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
Forsothe biyende Jordan, of the sones of Ruben, and of Gad, and of the half part of the lynage of Manasses, sixe scoore thousynde men, araied with armuris of batel.
38 Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
Alle these men werriouris and redi to batel camen with perfit herte in to Ebron, to make Dauid kyng on al Israel; but also alle the residue of Israel weren of oon herte, that Dauid schulde be maad king on al Israel.
39 Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
And thei weren ther at Dauid thre daies, and eten and drunken; for her britheren hadden maad redi to hem;
40 Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.
but also thei that weren niy hem, til to Isacar and Zabulon and Neptalym, brouyten looues on assis, and camelis, and mulis, and oxis, for to ete; mele, bundelis of pressid figis, dried grapis, wyn, oile, oxis and wetheres, to al plentee; for ioy was in Israel.

< 1 Tarihi 12 >