< 1 Tarihi 12 >

1 Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
And these [are] those coming to David at Ziklag, while shut up because of Saul son of Kish, and they [are] among the mighty ones, helping the battle,
2 suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
armed with bow, right and left handed, with stones, and with arrows, with bows, of the brothers of Saul, of Benjamin.
3 Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
The head [is] Ahiezer, and Joash, sons of Shemaab the Gibeathite, and Jeziel, and Pelet, sons of Azmaveth, and Berachah, and Jehu the Antothite,
4 da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
and Ishmaiah the Gibeonite, a mighty one among the thirty, and over the thirty, and Jeremiah, and Jahaziel, and Johanan, and Josabad the Gederathite.
5 Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
Eluzai, and Jerimoth, and Bealiah, and Shemariah, and Shephatiah the Haruphite;
6 Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
Elkanah, and Jesiah, and Azareel, and Joezer, and Jashobeam the Korahites,
7 da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
and Joelah, and Zebadiah, sons of Jeroham of Gedor.
8 Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
And of the Gadite there have been separated to David, to the fortress, to the wilderness, mighty men of valor, men of the host for battle, setting in array buckler and spear, and their faces [are as] the face of the lion, and as roes on the mountains for speed:
9 Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
Ezer the head, Obadiah the second, Eliab the third,
10 Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
Mishmannah the fourth, Jeremiah the fifth,
11 Attai na shida, Eliyel na bakwai,
Attai the sixth, Eliel the seventh,
12 Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
Johanan the eighth, Elzabad the ninth,
13 Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
Jeremiah the tenth, Machbannai the eleventh.
14 Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
These [are] of the sons of Gad, heads of the host; the least [is] one of one hundred, and the greatest, of one thousand;
15 Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
these [are] they who have passed over the Jordan in the first month—and it is full over all its banks—and cause all [those in] the valley to flee to the east and to the west.
16 Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
And [some] from the sons of Benjamin and Judah came to David at the stronghold,
17 Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
and David goes out before them, and answers and says to them, “If you have come to me for peace, to help me, I have a heart to unite with you; and if to betray me to my adversaries—without violence in my hands—the God of our fathers sees and reproves.”
18 Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
And the Spirit has clothed Amasai, head of the captains: “To you, O David, and with you, O son of Jesse—peace! Peace to you, and peace to your helper, for your God has helped you”; and David receives them, and puts them among the heads of the troop.
19 Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
And [some] from Manasseh have defected to David in his coming with the Philistines against Israel to battle—and they did not help them, for by counsel the princes of the Philistines sent him away, saying, “He defects with our heads to his master Saul.”
20 Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
In his going to Ziglag there have fallen to him from Manasseh: Adnah, and Jozabad, and Jediael, and Michael, and Jozabad, and Elihu, and Zillthai, heads of the thousands who [are] of Manasseh;
21 Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
and they have helped with David over the troop, for all of them [are] mighty men of valor, and they are captains in the host,
22 Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
for at that time, day by day, they come to David to help him, until it is a great camp, like a camp of God.
23 Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
And these [are] the numbers of the head, of the armed men of the host; they have come to David at Hebron to turn around the kingdom of Saul to him, according to the mouth of YHWH.
24 Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
The sons of Judah, carrying buckler and spear, [are] six thousand and eight hundred, armed ones of the host.
25 mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
Of the sons of Simeon, mighty men of valor for the host, [are] seven thousand and one hundred.
26 mutanen Lawi, su 4,600,
Of the sons of Levi [are] four thousand and six hundred;
27 haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
and Jehoiada [is] the leader of the Aaronite, and with him [are] three thousand and seven hundred,
28 da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
and Zadok, a young man, a mighty man of valor, and of the house of his father [are] twenty-two heads.
29 mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
And of the sons of Benjamin, brothers of Saul, [are] three thousand, and until now their greater part are keeping the charge of the house of Saul.
30 mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
And of the sons of Ephraim [are] twenty thousand and eight hundred, mighty men of valor, men of renown, according to the house of their fathers.
31 mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
And of the half of the tribe of Manasseh [are] eighteen thousand, who have been defined by name, to come to cause David to reign.
32 mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
And of the sons of Issachar, having understanding for the times, to know what Israel should do; their heads [are] two hundred, and all their brothers [are] at their command.
33 mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
Of Zebulun, going forth to the host, arranging battle with all instruments of battle, [are] fifty thousand, and keeping rank without a double heart.
34 mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
And of Naphtali, one thousand heads, and with them, with buckler and spear, [are] thirty-seven thousand.
35 mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
And of the Danite, arranging battle, [are] twenty-eight thousand and six hundred.
36 mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
And of Asher, going forth to the host, to arrange battle, [are] forty thousand.
37 kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
And from beyond the Jordan, of the Reubenite, and of the Gadite, and of the half of the tribe of Manasseh, with all instruments of the host for battle, [are] one hundred and twenty thousand.
38 Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
All these [are] men of war, keeping rank—they have come to Hebron with a perfect heart, to cause David to reign over all Israel, and also all the rest of Israel [are] of one heart, to cause David to reign,
39 Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
and they are there, with David, three days, eating and drinking, for their brothers have prepared for them.
40 Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.
And also those near to them—to Issachar, and Zebulun, and Naphtali—are bringing in bread on donkeys, and on camels, and on mules, and on oxen—food of fine flour, fig-cakes and grape-cakes, and wine, and oil, and oxen, and sheep, in abundance, for joy [is] in Israel.

< 1 Tarihi 12 >