< 1 Tarihi 11 >
1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Então todo o Israel se ajuntou a Davi em Hebrom, dizendo: Eis que nós somos teu osso e tua carne.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
E mesmo antes, quando Saul ainda era rei, tu conduzias as tropas de Israel. Também o SENHOR teu Deus te disse: Tu apascentarás o meu povo Israel, e tu serás líder do meu povo Israel.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Também vieram todos os anciãos de Israel ao rei em Hebrom, e Davi fez aliança com eles diante do SENHOR; e ungiram a Davi como rei sobre Israel, conforme a palavra do SENHOR por meio de Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
Então Davi e todo Israel foram a Jerusalém, a qual era Jebus, pois ali os jebuseus eram os moradores daquela terra.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
E os moradores de Jebus disseram a Davi: Tu não entrarás aqui. Porém Davi conquistou a fortaleza de Sião, que é a cidade de Davi.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
(Pois Davi havia dito: O primeiro a derrotar aos jebuseus será chefe e comandante. Então Joabe, filho de Zeruia, subiu primeiro, e foi feito comandante.)
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
E Davi habitou na fortaleza; por isso que foi chamada de cidade de Davi.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
E ele edificou a cidade ao redor, desde as fundações do aterro ao redor; e Joabe reparou o resto da cidade.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
E Davi ia cada vez mais crescendo em poder, pois o SENHOR dos exércitos era com ele.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Estes foram os líderes dos guerreiros que Davi teve, os que lhe deram forte apoio em seu reinado, com todo Israel, para o fazerem rei sobre Israel, conforme a palavra do SENHOR.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
E este é o número dos guerreiros que Davi teve: Jasobeão, filho de Hacmoni, chefe de capitães, o qual, fazendo uso de sua lança, matou trezentos de um vez.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
E depois dele Eleazar, filho de Dodô, o aoíta; ele era um dos três principais guerreiros.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
Este esteve com Davi em Pas-Damim, quando os filisteus se ajuntaram para a batalha; e havia ali uma plantação cheia de cevada. Enquanto o povo fugia dos filisteus,
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
Eles se puseram no meio da plantação, defenderam-na, e derrotaram os Filisteus; e o SENHOR lhes deu uma grande vitória.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
E três dos trinta comandantes desceram a Davi, na rocha junto à caverna de Adulão, enquanto o acampamento dos filisteus estava no vale de Refaim.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
E Davi estava então na fortaleza, enquanto havia uma tropa de filisteus em Belém.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
Davi teve um desejo, e disse: Quem me dera beber da água do poço de Belém, que está junto à porta!
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
E aqueles três irromperam pelo acampamento dos filisteus, e tiraram água do poço de Belém, que está junto à porta, tomaram dela, e a trouxeram a Davi. Davi, porém não a quis beber; em vez disso, derramou-a ao SENHOR,
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
E disse: Deus me proíba de fazer isto! Beberia eu o sangue destes homens com suas vidas? Pois eles arriscaram suas vidas para a trazerem. Por isso ele não a quis beber. Isto fizeram aqueles três guerreiros.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
E também Abisai, irmão de Joabe, foi o cabeça de três, o qual usando sua lança sobre trezentos, ele os matou; e foi famoso entre os três.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Dos três ele foi mais ilustre que os outros dois, por isso foi seu cabeça; porém não alcançou os três [primeiros].
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
[Também] Benaia, filho de Joiada, filho de homem valente, de grandes feitos, de Cabzeel; ele matou dois dos poderosos guerreiros de Moabe; ele também desceu, e matou um leão dentro de uma cova no tempo da neve.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
Ele também matou um homem egípcio alto, de cinco côvados; o egípcio trazia na mão uma lança como um lançador de tecelão; porém [Benaia] desceu a ele com um bastão; e arrancou a lança da mão do egípcio, e o matou com sua própria lança.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Estas coisas fez Benaia, filho de Joiada, e por isso foi famoso entre aqueles três guerreiros.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Eis que ele foi o mais ilustre dos trinta, mas não alcançou os três [primeiros]. E Davi o pôs sobre sua guarda pessoal.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
E os guerreiros dos exército foram: Asael, irmão de Joabe; Elanã filho de Dodô de Belém;
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Samote o harodita; Helez o pelonita;
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira, filho de Iques, o tecoíta; Abiezer o anatotita;
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Sibecai o husatita; Ilai o aoíta;
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maarai o netofatita; Helede, filho de Baaná, o netofatita;
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Itai, filho de Ribai, de Gibeá dos filhos de Benjamim; Benaia o piratonita;
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Hurai do ribeiro de Gaás; Abiel, o arbatita;
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Azmavete, o baarumita; Eliaba, o saalbonita;
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
Os filhos de Hasém, o gizonita; Jônatas, filho de Sage, o hararita;
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Aião filho de Sacar, o hararita; Elifal filho de Ur;
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Héfer, o mequeratita; Aías, o pelonita;
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hezro, o carmelita; Naarai, filho de Ezbai;
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joel, irmão de Natã; Mibar, filho de Hagri;
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Zeleque, o amonita; Naarai, o berotita, escudeiro de Joabe filho de Zeruia;
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira, o itrita; Garebe, o itrita;
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Urias, o heteu; Zabade, filho de Alai;
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina, filho de Siza, o rubenita, [o qual era] chefe dos rubenitas, e com ele trinta;
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanã, filho de Maaca; Josafá o mitenita;
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Uzia, o asteratia; Sama e Jeiel, filhos de Hotão, o aroerita;
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jedaiel, filho de Sinri, e seu irmão Joá, o tizita;
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Eliel, o maavita; Jeribai e Josavias, filhos de Elnaão; Itma, o moabita;
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel; Obede; e Jaasiel, o mezobaíta.