< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Tout Israël s’assembla auprès de David à Hébron, en disant: Voici, nous sommes tes os et ta chair.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
Autrefois déjà, même lorsque Saül était roi, c’était toi qui conduisais et qui ramenais Israël. L’Éternel, ton Dieu, t’a dit: Tu paîtras mon peuple d’Israël, et tu seras le chef de mon peuple d’Israël.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Ainsi tous les anciens d’Israël vinrent auprès du roi à Hébron, et David fit alliance avec eux à Hébron, devant l’Éternel. Ils oignirent David pour roi sur Israël, selon la parole de l’Éternel, prononcée par Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
David marcha avec tout Israël sur Jérusalem, qui est Jebus. Là étaient les Jébusiens, habitants du pays.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
Les habitants de Jebus dirent à David: Tu n’entreras point ici. Mais David s’empara de la forteresse de Sion: c’est la cité de David.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
David avait dit: Quiconque battra le premier les Jébusiens sera chef et prince. Joab, fils de Tseruja, monta le premier, et il devint chef.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
David s’établit dans la forteresse; c’est pourquoi on l’appela cité de David.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
Il fit tout autour de la ville des constructions, depuis Millo et aux environs; et Joab répara le reste de la ville.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
David devenait de plus en plus grand, et l’Éternel des armées était avec lui.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Voici les chefs des vaillants hommes qui étaient au service de David, et qui l’aidèrent avec tout Israël à assurer sa domination, afin de l’établir roi, selon la parole de l’Éternel au sujet d’Israël.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
Voici, d’après leur nombre, les vaillants hommes qui étaient au service de David. Jaschobeam, fils de Hacmoni, l’un des principaux officiers. Il brandit sa lance sur trois cents hommes, qu’il fit périr en une seule fois.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
Après lui, Éléazar, fils de Dodo, l’Achochite, l’un des trois guerriers.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
Il était avec David à Pas-Dammim, où les Philistins s’étaient rassemblés pour combattre. Il y avait là une pièce de terre remplie d’orge; et le peuple fuyait devant les Philistins.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
Ils se placèrent au milieu du champ, le protégèrent, et battirent les Philistins. Et l’Éternel opéra une grande délivrance.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Trois des trente chefs descendirent auprès de David sur le rocher dans la caverne d’Adullam, lorsque le camp des Philistins était dressé dans la vallée des Rephaïm.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
David était alors dans la forteresse, et il y avait un poste de Philistins à Bethléhem.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
David eut un désir, et il dit: Qui me fera boire de l’eau de la citerne qui est à la porte de Bethléhem?
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Alors les trois hommes passèrent au travers du camp des Philistins, et puisèrent de l’eau de la citerne qui est à la porte de Bethléhem. Ils l’apportèrent et la présentèrent à David; mais David ne voulut pas la boire, et il la répandit devant l’Éternel.
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
Il dit: Que mon Dieu me garde de faire cela! Boirais-je le sang de ces hommes qui sont allés au péril de leur vie? Car c’est au péril de leur vie qu’ils l’ont apportée. Et il ne voulut pas la boire. Voilà ce que firent ces trois vaillants hommes.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Abischaï, frère de Joab, était le chef des trois. Il brandit sa lance sur trois cents hommes, et les tua; et il eut du renom parmi les trois.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Il était le plus considéré des trois de la seconde série, et il fut leur chef; mais il n’égala pas les trois premiers.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Benaja, fils de Jehojada, fils d’un homme de Kabtseel, rempli de valeur et célèbre par ses exploits. Il frappa les deux lions de Moab. Il descendit au milieu d’une citerne, où il frappa un lion, un jour de neige.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
Il frappa un Égyptien d’une stature de cinq coudées et ayant à la main une lance comme une ensouple de tisserand; il descendit contre lui avec un bâton, arracha la lance de la main de l’Égyptien, et s’en servit pour le tuer.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Voilà ce que fit Benaja, fils de Jehojada; et il eut du renom parmi les trois vaillants hommes.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Il était le plus considéré des trente; mais il n’égala pas les trois premiers. David l’admit dans son conseil secret.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
Hommes vaillants de l’armée: Asaël, frère de Joab. Elchanan, fils de Dodo, de Bethléhem.
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Schammoth, d’Haror. Hélets, de Palon.
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira, fils d’Ikkesch, de Tekoa. Abiézer, d’Anathoth.
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Sibbecaï, le Huschatite. Ilaï, d’Achoach.
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maharaï, de Nethopha. Héled, fils de Baana, de Nethopha.
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Ithaï, fils de Ribaï, de Guibea des fils de Benjamin. Benaja, de Pirathon.
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Huraï, de Nachalé-Gaasch. Abiel, d’Araba.
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Azmaveth, de Bacharum. Éliachba, de Schaalbon.
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
Bené-Haschem, de Guizon. Jonathan, fils de Schagué, d’Harar.
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Achiam, fils de Sacar, d’Harar. Éliphal, fils d’Ur.
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Hépher, de Mekéra. Achija, de Palon.
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hetsro, de Carmel. Naaraï, fils d’Ezbaï.
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joël, frère de Nathan. Mibchar, fils d’Hagri.
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Tsélek, l’Ammonite. Nachraï, de Béroth, qui portait les armes de Joab, fils de Tseruja.
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira, de Jéther. Gareb, de Jéther.
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Urie, le Héthien. Zabad, fils d’Achlaï.
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina, fils de Schiza, le Rubénite, chef des Rubénites, et trente avec lui.
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanan, fils de Maaca. Josaphat, de Mithni.
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Ozias, d’Aschtharoth. Schama et Jehiel, fils de Hotham, d’Aroër.
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediaël, fils de Schimri. Jocha, son frère, le Thitsite.
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Éliel, de Machavim, Jeribaï et Joschavia, fils d’Elnaam. Jithma, le Moabite.
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Éliel, Obed et Jaasiel-Metsobaja.

< 1 Tarihi 11 >