< 1 Tarihi 11 >
1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Derpaa samlede hele Israel sig hos David i Hebron og sagde: »Vi er jo dit Kød og Blod!
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
Allerede før i Tiden, medens Saul var Konge, var det dig, som førte Israel ud i Kamp og hjem igen; og HERREN din Gud sagde til dig: Du skal vogte mit Folk Israel og være Hersker over mit Folk Israel!«
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Og alle Israels Ældste kom til Kongen i Hebron, og David sluttede i Hebron Pagt med dem for HERRENS Aasyn, og de salvede David til Konge over Israel efter HERRENS Ord ved Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
Derpaa drog David med hele Israel til Jerusalem, det er Jebus; der boede Jebusiterne, Landets oprindelige Indbyggere;
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
og Indbyggerne i Jebus sagde til David: »Her kan du ikke trænge ind!« Men David indtog Klippeborgen Zion, det er Davidsbyen.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
Og David sagde: »Den, der først slaar en Jebusit, skal være Øverste og Hærfører!« Og da Joab, Zerujas Søn, var den første, der steg derop, blev han Øverste.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
Saa tog David Bolig i Klippeborgen, hvorfor man kaldte den Davidsbyen;
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
og han befæstede Byen hele Vejen rundt fra Millo af; Resten af Byen genopførte Joab.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
Og David blev mægtigere og mægtigere; Hærskarers HERRE var med ham.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Følgende var de ypperste at Davids Helte, som sammen med hele Israel kraftig stod ham bi med at naa Kongedømmet, saa de fik ham valgt til Konge efter HERRENS Ord til Israel.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
Navnene paa Davids Helte var følgende: Isjba'al, Hakmonis Søn, Anføreren for de tre; det var ham, som engang svang sit Spyd over 300 faldne paa een Gang.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
Blandt de tre Helte kom efter ham Ahohiten El'azar, Dodos Søn;
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
han var med David ved Pas-Dammim, dengang Filisterne samlede sig der til Kamp. Marken var fuld af Byg, og Folkene flygtede for Filisterne;
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
men han stillede sig op midt paa Marken og holdt den og huggede Filisterne ned; og HERREN gav dem en stor Sejr.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Engang drog tre af de tredive ned til David paa Klippen, til Adullams Hule, medens Filisternes Hær var lejret i Refaimdalen.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
David var dengang i Klippeborgen, medens Filisternes Foged var i Betlehem.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
Saa vaagnede Lysten hos David, og han sagde: »Hvem skaffer mig en Drik Vand fra Cisternen ved Betlehems Port?«
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Da banede de tre Helte sig Vej gennem Filisternes Lejr, øste Vand af Cisternen ved Betlehems Port og bragte David det. Han vilde dog ikke drikke det, men udgød det for HERREN
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
med de Ord: »Gud vogte mig for at gøre det! Skulde jeg drikke de Mænds blod, som har vovet deres Liv? Thi med Fare for deres Liv har de hentet det!« Og han vilde ikke drikke det. Den Daad udførte de tre Helte.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Abisjaj, Joabs Broder, var Anfører for de tredive. Han svang sit Spyd over de faldne, og han var navnkundig blandt de tredive;
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
iblandt de tredive var han højt æret, og han var deres Anfører; men de tre naaede han ikke.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Benaja, Jojadas Søn, var en tapper Mand fra Kabze'el, der havde udført store Heltegerninger; han fældede de to Arielsønner fra Moab; og han steg ned og fældede en Løve i en Cisterne, en Dag den var faldet Sne.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
Ligeledes fældede han Ægypteren, en kæmpestor Mand, fem Alen høj. Ægypteren havde et Spyd som en Væverbom i Haanden, men han gik ned imod ham med en Stok, vristede Spydet ud af Haanden paa ham og dræbte ham med hans eget Spyd.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Disse Heltegerninger udførte Benaja, Jojadas Søn, og han var navnkundig iblandt de tredive Helte;
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
iblandt de tredive var han højt æret, men de tre naaede han ikke. David satte ham over sin Livvagt.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
De tapre Helte var: Asa'el, Joabs Broder; Elhanan, Dodos Søn, fra Betlehem;
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Haroriten Sjammot; Peloniten Helez;
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira, Ikkesj's Søn, fra Tekoa; Abiezer fra Anatot;
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Husjatiten Sibbekaj; Ahohiten Ilaj;
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maharaj fra Netofa; Heled, Ba'anas Søn, fra Netofa;
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Itaj, Ribajs Søn, fra det benjaminitiske Gibea; Benaja fra Pir'aton;
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Huraj fra Nahale-Ga'asj; Abiel fra Araba;
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Azmavet fra Bahurim; Sja'alboniten Eljaba;
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
Guniten Jasjen; Harariten Jonatan, Sjammas, Søn;
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Harariten Ahi'am, Sakars Søn; Elifal, Urs Søn;
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Mekeratiten Hefer; Peloniten Ahija;
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hezro fra Karmel; Na'araj, Ezbajs Søn;
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joel, Natans Broder; Mibhar, Hagritens Søn;
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Ammoniten Zelek; Naharaj fra Berot, der var Joabs, Zerujas Søns, Vaabendrager;
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira fra Jattir; Gareb fra Jattir;
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Hetiten Urias; Zabad, Alajs Søn;
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Rubeniten Adina, Sjizas Søn, et af Rubeniternes Overhoveder over tredive;
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanan, Ma'akas Søn; Mitniten Josjafat;
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Uzzija fra Asjtarot; Sjama og Je'uel, Aroeriten Hotams Sønner;
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediael, Sjimris Søn, og hans Broder Tiziten Joha;
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Mahaviten Eliel; Jeribaj og Josjavja, Elna'ams Sønner; Moabiten Jitma;
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel, Obed og Ja'asiel fra Zoba.