< 1 Tarihi 10 >

1 To, fa, Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa; Isra’ilawa kuwa suka gudu a gabansu, da yawa kuma suka mutu a kan Dutsen Gilbowa.
Filistliler İsrailliler'le savaşa tutuştu. İsrailliler Filistliler'in önünden kaçtı. Birçoğu Gilboa Dağı'nda ölüp yere serildi.
2 Filistiyawa suka matsa sosai suna bin Shawulu da’ya’yansa maza, suka kuma kashe’ya’yansa maza Yonatan, Abinadab da Malki-Shuwa.
Filistliler Saul'la oğullarının ardına düştüler. Saul'un oğulları Yonatan'ı, Avinadav'ı ve Malkişua'yı yakalayıp öldürdüler.
3 Yaƙin ya yi tsanani kewaye da Shawulu, kuma sa’ad da maharba suka rutsa shi, sai suka ji masa rauni.
Saul'un çevresinde savaş kızıştı. Derken Saul Filistli okçular tarafından vuruldu ve yaralandı.
4 Sai Shawulu ya ce wa mai riƙe masa kayan yaƙi, “Zare takobinka ka soke ni, in ba haka ba waɗannan marasa kaciya za su zo su yi mini ba’a.” Amma mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ji tsoro bai kuwa yi haka ba; saboda haka Shawulu ya zāre takobinsa ya fāɗi a kansa.
Saul silahını taşıyan adama, “Kılıcını çek de bana sapla” dedi, “Yoksa bu sünnetsizler gelip benimle alay edecekler.” Ama silah taşıyıcısı büyük bir korkuya kapılarak bunu yapmak istemedi. Bunun üzerine Saul kılıcını çekip kendini üzerine attı.
5 Da mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya fāɗi a kan takobinsa ya mutu.
Saul'un öldüğünü görünce, silah taşıyıcısı da kendini kılıcının üzerine atıp öldü.
6 Ta haka Shawulu da’ya’yansa maza uku suka mutu, dukan gidansa kuwa suka mutu tare.
Böylece Saul, üç oğlu ve bütün ev halkı birlikte öldüler.
7 Sa’ad da dukan Isra’ilawa a cikin kwari suka ga cewa mayaƙansu suna gudu, kuma cewa Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka zauna a cikinsu.
Vadide oturan İsrailliler, İsrail ordusunun kaçtığını, Saul'la oğullarının öldüğünü anlayınca, kentlerini terk edip kaçmaya başladılar. Filistliler gelip bu kentlere yerleştiler.
8 Kashegari, da Filistiyawa suka zo don su tuttuɓe waɗanda suka mutu, sai suka sami Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu a Dutsen Gilbowa.
Ertesi gün Filistliler, öldürülenleri soymak için geldiklerinde, Saul'la oğullarının Gilboa Dağı'nda öldüğünü gördüler.
9 Suka tuttuɓe shi suka yanke kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka kuma aika’yan aika ko’ina a ƙasar Filistiyawa, a yi shela labarin a cikin gumakansu da kuma mutanensu.
Saul'u soyduktan sonra başını kesip silahlarını aldılar. Sonra bu iyi haberi putlarına ve halka duyurmaları için Filist ülkesinin her yanına ulaklar gönderdiler.
10 Suka sa kayan yaƙinsa a haikalin allahnsu suka kuma rataye kansa a haikalin Dagon.
Saul'un silahlarını ilahlarının tapınağına koyup başını Dagon Tapınağı'na çaktılar.
11 Sa’ad da mazaunan Yabesh Gileyad suka ji dukan abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu,
Yaveş-Gilat halkı Filistliler'in Saul'a yaptıklarını duydu.
12 sai dukan jarumawa suka tafi suka ɗauki jikunan Shawulu da na’ya’yansa maza suka kawo Yabesh. Sa’an nan suka binne ƙasusuwan a ƙarƙashin babban itace oak a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
Bütün yiğitler gidip Saul'la oğullarının cesetlerini Yaveş'e getirdiler. Sonra kemiklerini Yaveş'teki yabanıl fıstık ağacının altına gömdüler ve yedi gün oruç tuttular.
13 Shawulu ya mutu domin rashin aminci ga Ubangiji; bai kiyaye maganar Ubangiji ba, ya ma nemi shawarar mace mai duba,
Saul RAB'be ihanet ettiği için öldü. RAB'bin sözünü yerine getirmedi. Yol göstermesi için RAB'be danışacağına bir cinciye danıştı. Bu yüzden RAB onu öldürdü. Krallığını da İşay oğlu Davut'a devretti.
14 bai kuwa nemi nufin Ubangiji ba. Saboda haka Ubangiji ya kashe shi, ya miƙa mulkin ga Dawuda ɗan Yesse.

< 1 Tarihi 10 >