< 1 Tarihi 10 >

1 To, fa, Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa; Isra’ilawa kuwa suka gudu a gabansu, da yawa kuma suka mutu a kan Dutsen Gilbowa.
فلسطینی‌ها با اسرائیلی‌ها وارد جنگ شدند و آنها را شکست دادند. اسرائیلی‌ها فرار کردند و در دامنهٔ کوه جلبوع تلفات زیادی به جای گذاشتند.
2 Filistiyawa suka matsa sosai suna bin Shawulu da’ya’yansa maza, suka kuma kashe’ya’yansa maza Yonatan, Abinadab da Malki-Shuwa.
فلسطینی‌ها شائول و سه پسر او یوناتان، ابیناداب و ملکیشوع را محاصره کردند و هر سه را کشتند.
3 Yaƙin ya yi tsanani kewaye da Shawulu, kuma sa’ad da maharba suka rutsa shi, sai suka ji masa rauni.
عرصه بر شائول تنگ شد و تیراندازان فلسطینی دورش را گرفتند و او را مجروح کردند.
4 Sai Shawulu ya ce wa mai riƙe masa kayan yaƙi, “Zare takobinka ka soke ni, in ba haka ba waɗannan marasa kaciya za su zo su yi mini ba’a.” Amma mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ji tsoro bai kuwa yi haka ba; saboda haka Shawulu ya zāre takobinsa ya fāɗi a kansa.
شائول به محافظ خود گفت: «پیش از اینکه به دست این کافرها بیفتم و رسوا شوم، تو با شمشیر خودت مرا بکش!» ولی آن مرد ترسید این کار را بکند. پس شائول شمشیر خودش را گرفته، خود را بر آن انداخت و مرد.
5 Da mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya fāɗi a kan takobinsa ya mutu.
محافظ شائول چون او را مرده دید، او نیز خود را روی شمشیرش انداخت و مرد.
6 Ta haka Shawulu da’ya’yansa maza uku suka mutu, dukan gidansa kuwa suka mutu tare.
شائول و سه پسر او با هم مردند و به این ترتیب خاندان سلطنتی شائول برافتاد.
7 Sa’ad da dukan Isra’ilawa a cikin kwari suka ga cewa mayaƙansu suna gudu, kuma cewa Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka zauna a cikinsu.
وقتی اسرائیلی‌های ساکن درهٔ یزرعیل شنیدند که سپاه اسرائیل شکست خورده و شائول و پسرانش کشته شده‌اند، شهرهای خود را ترک کردند و گریختند. آنگاه فلسطینی‌ها آمدند و در آن شهرها ساکن شدند.
8 Kashegari, da Filistiyawa suka zo don su tuttuɓe waɗanda suka mutu, sai suka sami Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu a Dutsen Gilbowa.
روز بعد که فلسطینی‌ها برای غارت کشته‌شدگان رفتند، جنازهٔ شائول و پسرانش را در کوه جلبوع پیدا کردند.
9 Suka tuttuɓe shi suka yanke kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka kuma aika’yan aika ko’ina a ƙasar Filistiyawa, a yi shela labarin a cikin gumakansu da kuma mutanensu.
آنها اسلحهٔ شائول را گرفتند و سر او را از تن جدا کرده، با خود بردند. سپس اسلحه و سر شائول را به سراسر فلسطین فرستادند تا خبر کشته شدن شائول را به بتها و مردم فلسطین برسانند.
10 Suka sa kayan yaƙinsa a haikalin allahnsu suka kuma rataye kansa a haikalin Dagon.
آنها اسلحهٔ شائول را در معبد خدایان خود گذاشتند و سرش را به دیوار معبد بت داجون آویختند.
11 Sa’ad da mazaunan Yabesh Gileyad suka ji dukan abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu,
وقتی ساکنان یابیش جلعاد شنیدند که فلسطینی‌ها چه بلایی بر سر شائول آورده‌اند،
12 sai dukan jarumawa suka tafi suka ɗauki jikunan Shawulu da na’ya’yansa maza suka kawo Yabesh. Sa’an nan suka binne ƙasusuwan a ƙarƙashin babban itace oak a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
مردان دلاور خود را فرستادند و ایشان جنازهٔ شائول و سه پسر او را به یابیش جلعاد آوردند و آنها را زیر درخت بلوط به خاک سپردند و یک هفته برای ایشان روزه گرفتند.
13 Shawulu ya mutu domin rashin aminci ga Ubangiji; bai kiyaye maganar Ubangiji ba, ya ma nemi shawarar mace mai duba,
مرگ شائول به سبب نافرمانی از خداوند و مشورت با احضارکنندهٔ ارواح بود.
14 bai kuwa nemi nufin Ubangiji ba. Saboda haka Ubangiji ya kashe shi, ya miƙa mulkin ga Dawuda ɗan Yesse.
او از خداوند هدایت نخواست و خداوند هم او را نابود کرد و سلطنتش را به داوود پسر یَسا داد.

< 1 Tarihi 10 >