< Ιουδα 1 >
1 ΙΟΥΔΑΣ δούλος Ιησού Χριστού, αδελφός δε Ιακώβου, προς τους κλητούς τους ηγιασμένους υπό Θεού Πατρός, και τετηρημένους υπό του Ιησού Χριστού
Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
2 έλεος πληθυνθείη εις εσάς, και ειρήνη, και αγάπη.
Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
3 Αγαπητοί, επειδή καταβάλλω πάσαν σπουδήν να σας γράψω περί της κοινής σωτηρίας, έλαβον ανάγκην να σας γράψω, προτρέπων εις το να αγωνίζησθε δια την πίστιν, ήτις άπαξ παρεδόθη εις τους αγίους.
Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
4 Διότι εισεχώρησαν λαθραίως τινές άνθρωποι, οίτινες ήσαν παλαιόθεν προγεγραμμένοι εις ταύτην την καταδίκην, ασεβείς, μεταστρέφοντες την χάριν του Θεού ημών εις ασέλγειαν, και αρνούμενοι τον μόνον δεσπότην Θεόν και Κύριον ημών Ιησούν Χριστόν.
Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
5 Θέλω δε να σας υπενθυμίσω, αν και σεις εγνωρίσατε ήδη τούτο, ότι ο Κύριος, αφού έσωσε τον λαόν εκ γης Αιγύπτου, απώλεσεν ύστερον τους μη πιστεύσαντας
Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
6 και αγγέλους οίτινες δεν εφύλαξαν την εαυτών αξίαν, αλλά κατέλιπον το ίδιον αυτών κατοικητήριον, εφύλαξε με παντοτεινά δεσμά υποκάτω του σκότους, δια την κρίσιν της μεγάλης ημέρας (aïdios )
Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios )
7 καθώς τα Σόδομα και τα Γόμορρα, και αι πέριξ αυτών πόλεις, εις την πορνείαν παραδοθείσαι κατά τον όμοιον με τούτους τρόπον, και ακολουθούσαι οπίσω άλλης σαρκός, πρόκεινται παράδειγμα τιμωρούμεναι με το αιώνιον πυρ. (aiōnios )
Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios )
8 Ομοίως και ούτοι ενυπνιαζόμενοι, την μεν σάρκα μιαίνουσι, την δε εξουσίαν καταφρονούσι, και τα αξιώματα βλασφημούσιν.
Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
9 Ο δε Μιχαήλ ο αρχάγγελος, ότε αγωνιζόμενος με τον διάβολον εφιλονείκει περί του σώματος του Μωϋσέως, δεν ετόλμησε να επιφέρη εναντίον αυτού κατηγορίαν βλάσφημον, αλλ' είπεν, Ο Κύριος να σε επιτιμήση.
Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
10 Ούτοι δε όσα μεν δεν εξεύρουσι βλασφημούσιν, όσα δε φυσικώς ως τα άλογα ζώα εξεύρουσιν, εις ταύτα φθείρονται.
Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
11 Ουαί εις αυτούς διότι περιεπάτησαν εις την οδόν του Κάϊν, και χάριν μισθού εξεχύθησαν εις την πλάνην του Βαλαάμ, και απωλέσθησαν εις την αντιλογίαν του Κορέ.
Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
12 Ούτοι είναι κηλίδες εις τας αγάπας σας, συμποσιάζοντες αφόβως, βόσκοντες εαυτούς, νεφέλαι άνυδροι υπό ανέμων περιφερόμεναι, δένδρα φθινοπωρινά άκαρπα, δις αποθανόντα, εκριζωθέντα,
Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
13 κύματα άγρια θαλάσσης επαφρίζοντα τας ιδίας αυτών αισχύνας, αστέρες πλανήται, δια τους οποίους το ζοφερόν σκότος είναι τετηρημένον εις τον αιώνα. (aiōn )
Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn )
14 Προεφήτευσε δε περί τούτων και ο Ενώχ, έβδομος από Αδάμ, λέγων, "Ιδού, ήλθεν ο Κύριος με μυριάδας αγίων αυτού,
Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
15 δια να κάμη κρίσιν κατά πάντων, και να ελέγξη πάντας τους ασεβείς εξ αυτών, δια πάντα τα έργα της ασεβείας αυτών, τα οποία έπραξαν και δια πάντα τα σκληρά τα οποία ελάλησαν κατ' αυτού αμαρτωλοί ασεβείς."
don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
16 Ούτοι είναι γογγυσταί, μεμψίμοιροι, περιπατούντες κατά τας επιθυμίας αυτών και το στόμα αυτών λαλεί υπερήφανα, και κολακεύουσι πρόσωπα χάριν ωφωλείας.
Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
17 Αλλά σεις, αγαπητοί, ενθυμήθητε τους λόγους τους προειρημένους υπό των αποστόλων του Κυρίου ημών Ιησού Χριστού,
Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
18 ότι σας έλεγον, ότι "εν εσχάτω καιρώ θέλουσιν είσθαι εμπαίκται, περιπατούντες κατά τας ασεβείς επιθυμίας αυτών."
Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
19 Ούτοι είναι οι αποχωρίζοντες εαυτούς, ζωώδεις, Πνεύμα μη έχοντες.
Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
20 Σεις όμως, αγαπητοί, εποικοδομούντες εαυτούς επί την αγιωτάτην πίστιν σας, προσευχόμενοι εν Πνεύματι Αγίω,
Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
21 φυλάξατε εαυτούς εις την αγάπην του Θεού, προσμένοντες το έλεος του Κυρίου ημών Ιησού Χριστού εις ζωήν αιώνιον. (aiōnios )
Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios )
22 Και άλλους μεν ελεείτε, κάμνοντες διάκρισιν,
Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
23 άλλους δε σώζετε μετά φόβου, αρπάζοντες αυτούς εκ του πυρός, μισούντες και τον χιτώνα τον μεμολυσμένον από της σαρκός.
ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
24 Εις δε τον δυνάμενον να σας φυλάξη απταίστους, και να σας στήση κατενώπιον της δόξης αυτού αμώμους εν αγαλλιάσει,
To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
25 εις τον μόνον σοφόν Θεόν τον σωτήρα ημών, είη δόξα και μεγαλωσύνη, κράτος και εξουσία, και νυν και εις πάντας τους αιώνας. Αμήν. (aiōn )
Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn )