< Προς Τιμοθεον Α΄ 6 >
1 Όσοι είναι υπό ζυγόν δουλείας, ας νομίζωσι τους κυρίους αυτών αξίους πάσης τιμής, διά να μη βλασφημήται το όνομα του Θεού και η διδασκαλία.
Duk waɗanda suke ƙarƙashin bauta, ya kamata su ɗauki iyayengijinsu a kan sun cancanci girmamawa matuƙa, don kada a ɓata sunan Allah da kuma koyarwarmu.
2 Οι δε έχοντες πιστούς κυρίους ας μη καταφρονώσιν αυτούς, διότι είναι αδελφοί, αλλά προθυμότερον ας δουλεύωσι, διότι είναι πιστοί και αγαπητοί οι απολαμβάνοντες την ευεργεσίαν. Ταύτα δίδασκε και νουθέτει.
Waɗanda suke da iyayengiji masu bi, to, kada su yi musu reni domin su’yan’uwa ne. A maimako, sai ma su fi bauta musu, saboda waɗanda suke cin moriyar hidimarsu masu bi ne, ƙaunatattu ne kuma a gare su. Waɗannan su ne abubuwan da za ka koya musu ka kuma gargaɗe su.
3 Εάν τις ετεροδιδασκαλή και δεν ακολουθή τους υγιαίνοντας λόγους του Κυρίου ημών Ιησού Χριστού και την διδασκαλίαν την κατ' ευσέβειαν,
In wani yana koyarwar ƙarya bai kuma yarda da sahihiyar koyarwar Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma koyarwa ta tsoron Allah ba,
4 είναι τετυφωμένος και δεν εξεύρει ουδέν, αλλά νοσεί περί συζητήσεις και λογομαχίας, εκ των οποίων προέρχεται φθόνος, έρις, βλασφημίαι, υπόνοιαι πονηραί,
yana cike da girman kai bai kuma san kome ba. Yana da mugun halin son gardama da muhawwara game da kalmomin da suke kawo kishi, rikici, maganar ƙeta, da mugayen zace-zace
5 μάταιαι συνδιαλέξεις ανθρώπων διεφθαρμένων τον νούν και απεστερημένων της αληθείας, νομιζόντων την ευσέβειαν ότι είναι πλουτισμός. Απομακρύνου από των τοιούτων.
da yawan tankiya tsakanin mutane masu mugun hali, waɗanda aka raba su da gaskiya, suke kuma tsammani cewa bin Allah wata hanya ce ta samun kuɗi.
6 Μέγας δε πλουτισμός είναι η ευσέβεια μετά αυταρκείας.
Amma bin Allah da gamsuwa riba ce mai yawa.
7 Διότι δεν εφέραμεν ουδέν εις τον κόσμον, φανερόν ότι ουδέ δυνάμεθα να εκφέρωμέν τι·
Gama ba mu zo duniya da kome ba, ba kuwa za mu fita daga cikinta da kome ba.
8 έχοντες δε διατροφάς και σκεπάσματα, ας αρκώμεθα εις ταύτα.
In dai muna da abinci da sutura, ai, sai mu gamsu da su.
9 Όσοι δε θέλουσι να πλουτώσι πίπτουσιν εις πειρασμόν και παγίδα και εις επιθυμίας πολλάς ανοήτους και βλαβεράς, αίτινες βυθίζουσι τους ανθρώπους εις όλεθρον και απώλειαν.
Mutanen da suke son yin arziki sukan fāɗi cikin jarraba, su fāɗa a tarko, suna mugayen sha’awace-sha’awace iri-iri na wauta da cutarwa, irin waɗanda suke dulmuyar da mutane, su kai ga lalacewa da hallaka.
10 Διότι ρίζα πάντων των κακών είναι η φιλαργυρία, την οποίαν τινές ορεγόμενοι απεπλανήθησαν από της πίστεως και διεπέρασαν εαυτούς με οδύνας πολλάς.
Gama son kuɗi shi ne tushen kowane irin mugun abu. Waɗansu mutane, don tsananin son kuɗi, sun bauɗe daga bangaskiya suka kuma jawo wa kansu da baƙin ciki iri-iri.
11 Συ όμως, ω άνθρωπε του Θεού, ταύτα φεύγε· ζήτει δε δικαιοσύνην, ευσέβειαν, πίστιν, αγάπην, υπομονήν, πραότητα.
Amma kai, mutumin Allah, ka guji duk wannan, ka kuma nemi adalci, tsoron Allah, bangaskiya, ƙauna, jimrewa da kuma hankali.
12 Αγωνίζου τον καλόν αγώνα της πίστεως· κράτει την αιώνιον ζωήν, εις την οποίαν και προσεκλήθης και ώμολόγησας την καλήν ομολογίαν ενώπιον πολλών μαρτύρων. (aiōnios )
Ka yi fama, kyakkyawar fama ta bangaskiya. Ka riƙi rai madawwamin nan, wanda aka kira saboda shi, sa’ad da ka yi kyakkyawar shaida a gaban shaidu masu yawa. (aiōnios )
13 Σε παραγγέλλω ενώπιον του Θεού του ζωοποιούντος τα πάντα και του Ιησού Χριστού του μαρτυρήσαντος ενώπιον του Ποντίου Πιλάτου την καλήν ομολογίαν,
Na umarce ka, a gaban Allah mai ba da rai ga kome, da kuma Kiristi Yesu wanda yayinda yake ba da shaida a gaban Buntus Bilatus ya yi kyakkyawar shaida,
14 να φυλάξης την εντολήν αμόλυντον, άμεμπτον, μέχρι της επιφανείας του Κυρίου ημών Ιησού Χριστού,
ka kiyaye wannan umarni ba tare da wani aibi ko abin zargi ba har yă bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi,
15 την οποίαν εν τοις ωρισμένοις καιροίς θέλει δείξει ο μακάριος και μόνος Δεσπότης, ο Βασιλεύς των βασιλευόντων, και Κύριος των κυριευόντων,
wanda Allah zai kawo a daidai lokaci, Allah, mai albarka wanda yake kaɗai Mai Mulki, Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji,
16 όστις μόνος έχει την αθανασίαν, κατοικών φως απρόσιτον, τον οποίον ουδείς των ανθρώπων είδεν ουδέ δύναται να ίδη· εις τον οποίον έστω τιμή και κράτος αιώνιον· αμήν. (aiōnios )
wanda shi kaɗai ne marar mutuwa wanda kuma yake zaune cikin hasken da ba ya kusatuwa, wanda babu wanda ya taɓa gani ko zai iya gani. A gare shi girma da iko su tabbata har abada. Amin. (aiōnios )
17 Εις τους πλουσίους του κόσμου τούτου παράγγελλε να μη υψηλοφρονώσι, μηδέ να ελπίζωσιν επί την αδηλότητα του πλούτου, αλλ' επί τον Θεόν τον ζώντα, όστις δίδει εις ημάς πλουσίως πάντα εις απόλαυσιν, (aiōn )
Ka umarci waɗanda suke da arziki a wannan duniya kada su ɗaga kai ko su sa begensu a kan dukiyar da ba ta da tabbaci, sai dai su sa begensu ga Allah, wanda yake ba mu kome a yalwace don jin daɗinmu. (aiōn )
18 να αγαθοεργώσι, να πλουτώσιν εις έργα καλά, να ήναι ευμετάδοτοι, κοινωνικοί,
Ka umarce su su yi nagarta, su wadatu cikin ayyuka nagari, su kuma zama masu bayarwa hannu sake da kuma masu niyyar yin taimako.
19 θησαυρίζοντες εις εαυτούς θεμέλιον καλόν εις το μέλλον, διά να απολαύσωσι την αιώνιον ζωήν.
Ta haka za su ajiye wa kansu dukiya a matsayin tushen mai ƙarfi don tsara mai zuwa, don su riƙi rai wanda yake na tabbatacce.
20 Ω Τιμόθεε, την παρακαταθήκην φύλαξον, αποστρεφόμενος τας βεβήλους ματαιολογίας και τας αντιλογίας της ψευδωνύμου γνώσεως,
Timoti, ka lura da abin da aka danƙa maka amana. Ka yi nesa da masu maganganun rashin tsoron Allah da kuma yawan mūsu da ake ƙarya, ake ce da shi ilimi,
21 την οποίαν τινές επαγγελλόμενοι επλανήθησαν κατά την πίστιν. Η χάρις είη μετά σού· αμήν.
wanda waɗansu suka furta kuma ta yin haka suka bauɗe daga bangaskiya. Alheri yă kasance tare da ku.