< Psalm 115 >

1 Nicht uns, Jehovah, nicht uns, sondern Deinem Namen gib Herrlichkeit, um Deiner Barmherzigkeit, um Deiner Wahrheit willen!
Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
2 Warum sollen die Völkerschaften sagen: Wo ist nun ihr Gott?
Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
3 Aber unser Gott ist in den Himmeln, Er kann tun, wozu Er Lust hat.
Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
4 Ihre Götzenbilder sind Silber und Gold, gemacht von den Händen des Menschen.
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
5 Einen Mund haben sie und reden nicht, Augen haben sie und sehen nicht;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
6 Ohren haben sie und hören nicht, eine Nase haben sie und riechen nicht;
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
7 Ihre Hände, und sie tasten nicht, ihre Füße, und sie gehen nicht, sie sprechen nicht aus ihrer Kehle.
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
8 Wie sie sind die, so sie machen, jeder, der auf sie vertraut.
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
9 Israel, vertraue auf Jehovah! Ihr Beistand und ihr Schild ist Er.
Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
10 Haus Aharons, vertrauet auf Jehovah; ihr Beistand und ihr Schild ist Er.
Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
11 Ihr, die ihr Jehovah fürchtet, vertrauet auf Jehovah; ihr Beistand und ihr Schild ist Er.
Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
12 Jehovah gedenkt unser, Er segnet: Er segnet das Haus Israel, Er segnet das Haus Aharons.
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13 Er segnet die, so Jehovah fürchten, die Kleinen mit den Großen.
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14 Jehovah wird zu euch hinzutun, zu euch und zu euren Söhnen.
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
15 Gesegnet seid ihr dem Jehovah, Der Himmel und Erde gemacht.
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16 Die Himmel, die Himmel sind Jehovahs, und die Erde gab Er den Söhnen des Menschen.
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17 Die Toten loben nicht Jah, noch alle, die zur Stille hinabfahren.
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18 Wir aber segnen Jah von nun an und bis in Ewigkeit. Hallelujah!
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.

< Psalm 115 >