< Jesaja 55 >
1 Auf! ein jeder, der dürstet, gehe hin zu den Wassern, und wer Silber nicht hat, gehet hin, kaufet und esset! und gehet, kaufet ohne Silber und ohne Kaufpreis, Wein und Milch.
“Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
2 Warum wäget ihr Silber dar für Nicht-Brot und eure Arbeit für etwas, das nicht sättigt? Hört, ja hört auf Mich und esset Gutes, und laben wird sich eure Seele an der Fettigkeit.
Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
3 Neigt euer Ohr und kommt zu Mir, hört, daß eure Seele lebe und Ich mit euch schließe einen Bund der Ewigkeit, die bewährte Barmherzigkeit Davids.
Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
4 Siehe, zum Zeugen für die Volksstämme gab Ich ihn, zum Führer und Gebieter den Volksstämmen.
Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
5 Siehe, rufen wirst du eine Völkerschaft, die du nicht kennst, und eine Völkerschaft, die dich nicht kannte, wird zu dir laufen, um Jehovahs, deines Gottes willen und wegen des Heiligen Israels, weil Er dich verklärt.
Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
6 Suchet nach Jehovah, da Er zu finden ist, rufet Ihn an, da Er nahe ist.
Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
7 Der Ungerechte verlasse seinen Weg und der Mann des Unrechts seine Gedanken und kehre zu Jehovah zurück, und Er wird Sich sein erbarmen, und zu unserem Gott, weil Er viel vergibt.
Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
8 Denn Meine Gedanken sind nicht eure Gedanken und eure Wege sind nicht Meine Wege, spricht Jehovah.
“Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
9 Denn die Himmel sind höher denn die Erde, so sind Meine Wege höher denn eure Wege, und Meine Gedanken denn eure Gedanken.
“Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
10 Denn wie der Platzregen und der Schnee herab vom Himmel kommt und nicht dahin zurückkehrt, vielmehr die Erde netzt und sie hervorbringen und sprossen läßt, und Samen gibt dem, der sät, und Brot dem, der da ißt:
Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
11 So wird Mein Wort sein, das von Meinem Mund ausgeht. Nicht kehrt es leer zu Mir zurück, sondern tut das, woran Ich Lust habe, und läßt gelingen, wozu Ich es gesandt.
haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
12 Denn ihr zieht aus in Fröhlichkeit und werdet geleitet im Frieden; die Berge und die Hügel brechen in Jubelsang aus vor euch, und alle Bäume des Gefildes klatschen mit der Hand.
Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
13 Statt des Dorngebüsches steigt auf die Tanne, statt des Stechdorns steigt auf die Myrte und soll für Jehovah zum Namen und zum ewigen Zeichen sein, das nicht wird ausgerottet.
A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”