< Hesekiel 13 >
1 Und es geschah das Wort Jehovahs an mich, sprechend:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Menschensohn, weissage über die Propheten Israels, die da weissagen, und sprich zu denen, die aus ihrem Herzen weissagen: Hört das Wort Jehovahs.
“Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
3 So spricht der Herr Jehovah: Wehe über die törichten Propheten, die nach ihrem Geiste gehen und dem, was sie nicht sahen.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
4 Wie Füchse in den Öden sind, Israel, deine Propheten geworden.
Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
5 Ihr stieget nicht hinauf in die Durchbrüche, noch zäuntet ihr einen Zaun für das Haus Israel, zu stehen im Streit am Tag Jehovahs.
Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
6 Sie schauen Eitles und wahrsagen Falsches, sie sprechen: Jehovahs Spruch! und Jehovah hat sie nicht gesandt, und lassen darauf warten, daß Er das Wort bestätige.
Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
7 Habt ihr nicht ein eitel Gesicht geschaut, falsche Wahrsagungen gesprochen? und ihr sprechet: Jehovahs Spruch! und Ich habe nicht geredet.
Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
8 Darum spricht so der Herr Jehovah: Weil ihr Eitles redet und Falsches schaut, darum sehet, bin Ich wider euch, spricht der Herr Jehovah.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Und Meine Hand soll sein wider die Propheten, die Eitles schauen und Falsches wahrsagen. Im Kreise Meines Volkes sollen sie nicht sein und nicht eingeschrieben in die Schrift des Hauses Israels und nicht kommen auf den Boden Israels, auf daß ihr wisset, daß Ich der Herr Jehovah bin.
Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
10 Weil und alldieweil sie Mein Volk verleiten und sprechen: Friede! und ist kein Friede. Und baut es eine Scheidemauer - sie übertünchen sie mit Untauglichem.
“‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
11 Sprich zu den Tünchern mit dem Untauglichen: Sie falle! Ein überflutender Platzregen ist da, und ihr, Steine des Hagels, sollet fallen, und ein Wind des Wettersturmes soll sie durchbrechen.
saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
12 Und siehe, die Wand fällt. Wird man nicht zu euch sagen: Wo ist die Tünche, mit der ihr habt getüncht?
Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
13 Darum, so spricht der Herr Jehovah, lasse Ich den Wind des Wettersturmes durchbrechen in Meinem Grimm, und ein überflutender Platzregen kommt in Meinem Zorn, und Steine des Hagels im Grimm zur Vollendung.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
14 Und reiße nieder die Wand, die ihr mit Untauglichem getüncht, und bringe sie zur Erde danieder, daß ihre Grundfeste aufgedeckt wird, und sie fällt, daß ihr alle werdet in ihrer Mitte; auf daß ihr wisset, daß Ich Jehovah bin.
Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Und Ich vollende Meinen Grimm an der Wand, und an denen, die mit dem Untauglichem sie getüncht haben, und spreche zu euch: Nicht mehr ist die Mauer, und nicht mehr die, die so übertünchten.
Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
16 Die Propheten Israels, die über Jerusalem weissagten, und die Schauer, die für sie Frieden schauten, und ist kein Frieden, spricht der Herr Jehovah.
waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
17 Du aber, Menschensohn, richte dein Angesicht auf deines Volkes Töchter, die da aus ihrem Herzen weissagen, und weissage über sie!
“To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
18 Und sprich: So spricht der Herr Jehovah: Wehe euch, die ihr Kissen nähet an alle Gelenke der Hände, und Kopftücher für Köpfe jeglichen Wuchses machet, um Seelen zu erjagen. - Die Seelen erjaget ihr Meinem Volk, und erhaltet euch Seelen am Leben.
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
19 Und ihr entweiht Mich bei Meinem Volke für eine Handvoll Gerste und für Bissen Brotes, damit, daß ihr Seelen zum Tode bringt, die nicht sterben sollten, und am Leben erhaltet Seelen, die nicht leben sollten, damit, daß ihr täuschet Mein Volk, die, so auf Falsches hören.
Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
20 Darum, so spricht der Herr Jehovah, siehe, Ich will an eure Kissen, womit ihr die Seelen jaget, daß sie entfliegen. Aber Ich reiße sie ab von euren Armen und entsende die Seelen, die ihr jagtet, - die Seelen, daß sie entfliegen.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
21 Und Ich zerreiße eure Kopftücher und errette Mein Volk aus eurer Hand, daß sie nicht mehr in eurer Hand als Erjagtes sind, und ihr wisset, daß Ich Jehovah bin.
Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
22 Weil ihr durch Lüge des Gerechten Herz verzagen lasset, dem Ich nicht wehe tun will, und ihr stärket die Hände des Ungerechten, daß er von seinem bösen Weg nicht umkehre und am Leben bleibe.
Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
23 Darum sollt ihr nicht Eitles schauen, und Wahrsagung nicht weiter wahrsagen. Und Ich errette Mein Volk aus eurer Hand, daß ihr wisset, daß Ich Jehovah bin.
saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”