< 2 Koenige 25 +
1 Und es geschah im neunten Jahre seines Königtums, im zehnten Monat am zehnten des Monats, kam Nebuchadnezzar, der König von Babel, er und all seine Streitmacht wider Jerusalem, und lagerte sich wider sie und bauten ein Bollwerk auf wider sie ringsumher.
A rana ta goma ga wata na goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya ne Nebukadnezzar sarkin Babilon tare da dukan rundunan yaƙinsa, ya tasam wa Urushalima. Ya yi sansani a bayan birnin, ya kewaye ta da shirin yaƙi.
2 Und die Stadt kam in Belagerung bis ins elfte Jahr des Königs Zidkijahu.
Haka birnin ta kasance a kewaye har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
3 Am neunten des Monats war die Hungersnot in der Stadt stark geworden, und es war kein Brot für das Volk des Landes:
A rana ta tara ta watan huɗu, lokacin da yunwa ta yi tsanani a birnin, babu kuma abinci domin mutane su ci.
4 Und die Stadt ward erbrochen und alle Männer des Streites bei Nacht des Weges durch das Tor zwischen den zwei Stadtmauern am Garten des Königs, und die Chaldäer waren wider die Stadt ringsumher. Er aber ging des Weges nach dem Blachfelde.
Sai aka huda katanga sa’an nan dukan sojoji suka tsere da dare a ƙofa tsakanin katanga biyu da suke kusa da lambun sarki, ko da yake Babiloniyawa sun kewaye birnin. Suka tsere suka nufi Araba.
5 Aber die Streitmacht der Chaldäer setzte hinter dem König nach und holten ihn ein auf dem Blachfeld von Jericho, und seine ganze Streitmacht zerstreute sich von ihm.
Amma sojojin Babiloniyawa suka bi sarki, suka cin masa a filayen Yeriko. Dukan sojojinsa kuwa suka rabu da shi suka watse.
6 Und sie erfaßten den König und brachten ihn hinauf zum König von Babel nach Riblath, und sie redeten mit ihm im Gericht.
Aka kama shi, aka kai shi gaban sarkin Babilon a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.
7 Und die Söhne Zidkijahus schlachteten sie vor seinen Augen, und dem Zidkijahu blendete er die Augen und band ihn in zwei Erzfesseln und brachte ihn hinein nach Babel.
Suka kashe’ya’yan Zedekiya a gabansa, sa’an nan aka ƙwaƙule idanunsa. Suka daure shi da sarƙar tagulla, suka kai shi Babilon.
8 Und im fünften Monat, am siebenten des Monats, das ist das neunzehnte Jahr der Jahre Nebuchadnezzars, König von Babel, kam Nebusaradan, der Oberste der Leibwachen, ein Knecht des Königs von Babel, nach Jerusalem;
A rana ta bakwai na watan biyar, wadda ta zama shekara ta goma sha tara ta mulkin Sarki Nebukadnezzar na Babilon, Nebuzaradan, babban hafsan matsaran sarki, kuma bafadan sarkin Babilon, ya zo Urushalima
9 Und er verbrannte das Haus Jehovahs und das Haus des Königs und alle Häuser Jerusalems, und jegliches große Haus verbrannte er mit Feuer.
Ya cinna wa haikalin Ubangiji wuta, da fadan sarki, da kuma dukan gidajen Urushalima. Ya kuma ƙone duk wani gini mai muhimmanci.
10 Und die Stadtmauern Jerusalems ringsumher riß die ganze Streitmacht der Chaldäer mit dem Obersten der Leibwachen ein.
Dukan mayaƙan Babilon a ƙarƙashin umarnin babban hafsan matsaran sarki, suka rushe katangar Urushalima.
11 Und das übrige Volk, das in der Stadt verblieben war, und die Abgefallenen, die zum König von Babel abfielen, und die übrige Menge führte Nebusaradan, der Oberste der Leibwache weg.
Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
12 Und von den Armen des Landes ließ der Oberste der Leibwachen verbleiben zu Weingärtnern und Ackerleuten.
Amma hafsan ya bar waɗansu daga cikin mafiya talauci na ƙasar don su yi aiki a lambunan inabi da kuma gonaki.
13 Die ehernen Säulen aber am Hause Jehovahs und die Gestelle und das eherne Meer im Hause Jehovahs zerbrachen die Chaldäer und brachten das Erz davon nach Babel.
Babiloniyawan kuma suka sassare ginshiƙan tagulla, da wuraren zama da za a iya matsar da su, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla da yake a haikalin Ubangiji, suka kwashe tagullan zuwa Babilon.
14 Und die Töpfe und die Schaufeln und die Messer und die Pfannen und alle ehernen Gefäße, womit man Dienst tat, nahmen sie.
Suka ɗauke tukwane, da manyan cokula, da acibalbal, da kwanoni, da dai dukan kayan da aka yi da tagulla don hidima a haikalin Ubangiji.
15 Und auch die Räuchpfannen und die Sprengbecken, was von Gold war, das Gold, und was von Silber war, das Silber, nahm der Oberste der Leibwachen.
Babban hafsan matsaran sarkin ya kwashe har da kwanoni na kwashe garwashin wuta da sauran kwanoni, dukansu kuwa ƙeran zinariya ko azurfa tsatsa ne.
16 Die zwei Säulen, das eine Meer und die Gestelle, die Salomoh für das Haus Jehovahs gemacht - das Erz aller dieser Geräte war nicht zu wägen.
Tagullar ginshiƙai biyun nan, da ta ƙaton kwanon da ake ce da shi Teku, da ta dukan amalanke masu riƙe ruwa waɗanda Sarki Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji, sun fi gaba a auna su.
17 Achtzehn Ellen hoch war die eine Säule, und ein Knauf darauf von Erz, und der Knauf drei Ellen hoch, und ein Flechtwerk und Granatäpfel rings an dem Knauf, alles von Erz, und ebenso an der zweiten Säule am Flechtwerk.
Tsawon kowane ginshiƙi, ƙafa ashirin da bakwai ne. Hulunan tagullan da suke ƙwalƙwalin kowane ginshiƙi kuma yana da tsawon ƙafa huɗu da rabi. Kuma aka yi masa ado da saƙa da’ya’yan itace kewaye da shi. Bayan ginshiƙin ma haka yake.
18 Und der Oberste der Leibwachen nahm Serajah, den Hauptpriester, und Zephanjahu, den zweiten Priester, und drei Hüter der Schwelle.
Babban hafsan ya kwashi Serahiya babban firist, da Zefaniya na biye da shi a girma, da matsara ƙofofi uku.
19 Und aus der Stadt nahm er einen Hofbeamten, der über die Kriegsleute bestellt war, und fünf Männer, die das Angesicht des Königs sahen, die in der Stadt gefunden wurden, und den Schreiber des Obersten des Heeres, der das Volk des Landes zum Heere aushob, und sechzig Mann vom Volke des Landes, die in der Stadt gefunden wurden.
Daga cikin waɗanda suka rage a birnin, ya ɗauki hafsa mai kula da dakaru, da kuma mashawartan sarki guda biyar. Ya kuma tafi da magatakarda wanda yake babban jami’in soja mai ɗaukan dukan jama’an ƙasar, tare da mutanensa guda sittin waɗanda aka samu a birnin.
20 Und Nebusaradan, der Oberste der Leibwachen, nahm sie und brachte sie zum König von Babel nach Riblath.
Nebuzaradan, babban hafsan, ya kwashe su duka ya kawo su wurin sarkin Babilon a Ribla.
21 Und der König von Babel schlug sie und tötete sie in Riblath im Lande Chamath, und Judah ward von seinem Boden weggeführt.
A can Ribla, a ƙasar Hamat, sarkin Babilon ya sa aka kashe su. Haka Yahuda ta tafi bauta daga ƙasarta.
22 Und anlangend das Volk, das im Lande Judah verblieben war, das Nebuchadnezzar, der König von Babel, zurückließ; über sie bestellte er Gedaljahu, den Sohn Achikams, des Sohnes Schaphans.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zaɓi Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan yă zama shugaban sauran mutanen da suka rage a Yahuda.
23 Und es hörten alle Obersten der Streitmächte, sie und ihre Mannen, daß der König von Babel Gedaljahu bestellt hätte, und kamen zu Gedaljahu nach Mizpah. Und Jischmael, der Sohn Nethanjahs, und Jochanan, Kareachs Sohn, und Seraja, der Sohn Tanchumeths, des Netophiters, und Jaasanjahu, der Sohn des Maachathi, sie und ihre Mannen.
Sa’ad da dukan hafsoshin soja tare da mutanensu suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya a matsayin gwamna, sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Mutanen da suka zo su ne, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan ɗan Kareya, Serahiya ɗan Tanhumet mutumin Netofa, Ya’azaniya ɗan mutumin Ma’aka, tare da mutanensu.
24 Und Gedaljahu schwur ihnen und ihren Mannen und sprach zu ihnen: Fürchtet euch nicht vor den Knechten der Chaldäer. Wohnet im Land und dienet dem König von Babel, so wird es euch wohl gehen.
Gedaliya ya tabbatar musu da rantsuwa cewa, “Kada ku ji tsoron jama’ar Babiloniyawa, muddin kun zauna lafiya, kun kuma bauta wa sarkin Babilon, kome zai yi muku kyau.”
25 Und es geschah im siebenten Monat, daß Ischmael, Nethanjahs Sohn, des Sohnes Elischamas, von königlichem Samen, kam, und zehn Männer mit ihm, und sie schlugen Gedal- jahu, daß er starb, und die Juden und die Chaldäer, die mit ihm waren in Mizpah.
Amma a wata na bakwai, sai Ishmayel, ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake daga gidan sarauta, ya zo tare da mutane goma, suka kashe Gedaliya duk da mutanen Yahuda, da na Babilon da suke tare da shi na Mizfa.
26 Und es machte sich alles Volk, vom Kleinen bis zum Großen, und auch die Obersten der Streitmächte auf, und gingen nach Ägypten; denn sie fürchteten sich vor den Chaldäern.
Ganin haka sai dukan mutane, babba da ƙarami, tare da shugabannin sojoji, suka tashi suka gudu zuwa ƙasar Masar, gama suna tsoron mutanen Babilon.
27 Und es geschah im siebenunddreißigsten Jahre der Wegführung Jehojachins, des Königs von Judah, im zwölften Monat am siebenundzwanzigsten des Monats, erhob Evil Merodach, König von Babel, im Jahre, da er König ward, das Haupt Jeojachins des Königs von Judah aus dem Hause des Kerkers,
A shekara ta talatin da bakwai ta bautar Yehohiyacin sarkin Yahuda, a shekaran da Ewil-Merodak ya ci sarautan Babilon, sai ya saki Yehohiyacin daga jaru, ya sake shi a rana ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu.
28 Und redete Gutes mit ihm und setzte seinen Thron über den Thron der Könige, die bei ihm in Babel waren.
Ya yi wa Yehohiyacin maganar alheri, ya kuma ɗaukaka shi sama da sauran sarakunan da suke tare da shi a Babilon.
29 Und veränderte die Kleider seines Kerkers und er aß das Brot beständig vor ihm alle Tage seines Lebens.
Don haka Yehohiyacin ya tuɓe kayan fursuna. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har iyakar ransa.
30 Auch wurde ihm sein Unterhalt, ein beständiger Unterhalt vom Könige gegeben, der Betrag eines Tages an seinem Tag, alle Tage seines Lebens.
Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.