< Psalm 89 >
1 Eine Unterweisung. Von Etan, dem Esrachiten: Die Gnadenerweisungen des HERRN will ich ewiglich besingen und seine Wahrheit mit meinem Munde verkündigen von Geschlecht zu Geschlecht.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Und zwar sage ich: Auf ewig wird die Gnade gebaut, in den Himmeln bestätigst du deine Treue:
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 «Ich habe mit meinem Auserwählten einen Bund geschlossen, habe meinem Knecht David geschworen:
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 Auf ewig will ich deinen Samen bestätigen und für alle Geschlechter bauen deinen Thron!» (Pause)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 Und die Himmel werden deine Wundertat preisen, o HERR, ja, deine Treue in der Gemeinde der Heiligen!
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Denn wer in den Wolken ist dem HERRN zu vergleichen, wer ist dem HERRN ähnlich unter den Göttersöhnen?
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 Gott ist sehr schrecklich im Kreise der Heiligen und furchtbar über alle um ihn her.
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 HERR, Gott der Heerscharen, wer ist mächtig wie du? Und deine Treue ist um dich her!
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Du herrschest über das stolze Meer; wenn sich seine Wellen erheben, so glättest du sie.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Du hast Rahab wie einen Erschlagenen zermalmt, mit deinem starken Arm zerstreutest du deine Feinde.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 Dein ist der Himmel, dir gehört auch die Erde, der Weltkreis und was ihn erfüllt; du hast es alles gegründet.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 Norden und Süden hast du erschaffen, Tabor und Hermon jauchzen ob deines Namens.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Du hast einen Arm voll Kraft, stark ist deine Hand, hoch erhoben deine Rechte.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 Recht und Gerechtigkeit sind deines Thrones Feste, Gnade und Treue gehen vor deinem Angesicht her.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Wohl dem Volk, das den Jubelschall kennt! O HERR, im Lichte deines Angesichts werden sie wandeln.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 Ob deines Namens frohlocken sie allezeit und sind erhoben durch deine Gerechtigkeit;
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 denn du bist ihr mächtiger Ruhm und durch deine Huld wird unser Horn erhöht.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 Denn vom HERRN kommt unser Schild und vom Heiligen Israels unser König.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Damals redetest du durch ein Gesicht mit deinen Frommen und sprachst: «Ich habe die Hilfe einem Helden übertragen, einen Auserwählten aus dem Volk erhöht;
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 ich habe meinen Knecht David gefunden und ihn mit meinem heiligen Öl gesalbt;
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 meine Hand soll beständig mit ihm sein, und mein Arm soll ihn stärken.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 Kein Feind soll ihn überlisten und kein Ruchloser ihn unterdrücken;
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 sondern ich will seine Widersacher vor ihm zermalmen und seine Hasser schlagen;
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 aber meine Treue und Gnade sollen mit ihm sein, und in meinem Namen soll sein Horn sich erheben.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 Und ich will seine Hand ins Meer tauchen und seine Rechte in die Ströme.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 Er wird zu mir rufen: Du bist mein Vater, mein Gott und der Fels meines Heils.
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Und ich will ihn zum Erstgeborenen machen, zum Höchsten der Könige auf Erden.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 Auf ewig bewahre ich ihm meine Gnade, und mein Bund soll ihm festbleiben.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 Und ich setze seinen Samen auf ewig ein und mache seinen Thron wie die Tage des Himmels.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Wenn seine Söhne mein Gesetz verlassen und nicht in meinen Verordnungen wandeln,
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 wenn sie meine Satzungen entheiligen und meine Gebote nicht beachten,
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 so will ich ihre Sünden mit der Rute heimsuchen und ihre Missetat mit Schlägen;
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 aber meine Gnade will ich ihm nicht entziehen und meine Treue nicht verleugnen;
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 meinen Bund will ich nicht ungültig machen und nicht ändern, was über meine Lippen gekommen ist.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 Einmal habe ich bei meiner Heiligkeit geschworen; sollte ich David belügen?
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 Sein Same soll ewig bleiben und sein Thron wie die Sonne vor mir;
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 wie der Mond soll er ewig bestehen und wie der Zeuge in den Wolken zuverlässig sein!» (Pause)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Und doch hast du verstoßen und verworfen und bist zornig geworden über deinen Gesalbten!
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Du verachtest den Bund deines Knechtes und trittst seine Krone zu Boden;
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 du hast alle seine Mauern zerrissen und seine Festungen in Trümmer gelegt;
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 es berauben ihn alle, die vorüberziehen, er ist seinen Nachbarn zum Gespött;
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 du hast die rechte Hand seiner Widersacher erhöht, hast allen seinen Feinden Freude gemacht;
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 du ließest zurückweichen sein scharfes Schwert und schenktest ihm keinen Sieg im Krieg;
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 du hast seinem Glanz ein Ende gemacht und seinen Thron zu Boden gestürzt;
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 du hast die Tage seiner Jugend verkürzt und ihn mit Schande bedeckt. (Pause)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 Wie lange, o HERR, willst du dich so verbergen? Soll dein Zorn stets wie Feuer brennen?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Gedenke mein! Was ist das Leben? Warum willst du alle Menschenkinder vergeblich erschaffen haben?
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 Wo ist einer, der den Tod nicht sähe und seine Seele erretten könnte von des Totenreichs Gewalt? (Pause) (Sheol )
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol )
49 Wo sind, o Herr, deine frühern Gnadenerweise, die du dem David in deiner Treue zugeschworen hast?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Gedenke, o Herr, der Schmach, die deinen Knechten angetan wird, daß ich in meinem Busen den Hohn der vielen Völker trage,
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 womit deine Feinde dich, HERR, schmähen, womit sie schmähen die Fußstapfen deines Gesalbten!
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Gepriesen sei der HERR ewiglich! Amen, Amen!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!