< Psalm 81 >
1 Dem Vorsänger. Auf der Gittit. Von Asaph. Jubelt Gott, der unsre Stärke ist, jauchzet dem Gott Jakobs!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Stimmt ein Lied an und nehmt die Pauke zur Hand, die liebliche Harfe mit dem Psalter!
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Blaset am Neumond die Posaune, am Vollmond, unserm festlichen Tag!
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 Denn das ist Israels Pflicht; der Gott Jakobs hat ein Anrecht darauf.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 Er verordnete es zum Zeugnis in Joseph, als er auszog wider Ägypten.
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 Eine Sprache, die ich nicht kannte, hörte ich: «Ich habe die Last von seiner Schulter genommen, seine Hände sind des Tragkorbes los geworden.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 Da du mich anriefst in der Not, errettete ich dich; ich antwortete dir mit geheimnisvoller Donnerstimme und prüfte dich am Haderwasser. (Pause)
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 Höre, mein Volk, ich will dich ermahnen; Israel, wenn du mir doch Gehör schenken wolltest!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 Kein fremder Gott soll unter dir sein, und einen unbekannten Gott bete nicht an!
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 Ich bin der HERR, dein Gott, der dich aus Ägyptenland heraufgeführt hat. Tue deinen Mund weit auf, so will ich ihn füllen!
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 Aber mein Volk hat meiner Stimme nicht gehorcht, und Israel wollte nichts von mir.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 Da überließ ich sie der Verstocktheit ihres Herzens, daß sie wandelten nach ihrem eigenen Rat.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 Wollte mein Volk mir gehorchen und Israel in meinen Wegen wandeln,
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 wie leicht könnte ich ihre Feinde demütigen und meine Hand gegen ihre Widersacher wenden!
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 Die den HERRN hassen, müßten ihm schmeicheln; ihre Zeit aber würde ewiglich währen!
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 Und er würde sie mit dem besten Weizen speisen und mit Honig aus dem Felsen sättigen!»
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”