< Psalm 21 >
1 Dem Vorsänger. Ein Psalm Davids. O HERR, es freut sich der König in deiner Kraft, und wie frohlockt er so sehr ob deinem Heil!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
2 Du hast ihm gegeben, was sein Herz wünschte, und ihm nicht verweigert, was seine Lippen begehrten. (Pause)
Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
3 Denn du begegnetest ihm mit köstlichen Segnungen, du setztest eine goldene Krone auf sein Haupt.
Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
4 Er bat dich um Leben, da gabst du es ihm, Verlängerung der Tage immer und ewiglich.
Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
5 Er hat große Ehre durch dein Heil; du legst Hoheit und Pracht auf ihn;
Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
6 denn du setzest ihn zum Segen für immer, erquickst ihn mit Freude durch dein Angesicht.
Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
7 Denn der König vertraut auf den HERRN, und durch die Gnade des Höchsten wird er nicht wanken.
Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
8 Deine Hand wird alle deine Feinde finden, deine Rechte wird finden deine Hasser.
Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
9 Du wirst sie machen wie einen feurigen Ofen zur Zeit deines Erscheinens, der HERR wird sie in seinem Zorn verschlingen, das Feuer wird sie fressen.
A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
10 Ihre Frucht wirst du vom Erdboden vertilgen und ihren Samen unter den Menschenkindern.
Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
11 Denn sie hegen Arges wider dich, sie schmieden Pläne, die sie nicht ausführen können.
Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
12 Denn du machst, daß sie den Rücken zeigen; mit deiner Bogensehne zielst du gegen ihr Angesicht.
gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
13 Erhebe dich, HERR, in deiner Kraft, so wollen wir singen und preisen deine Stärke!
Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.