< Psalm 132 >
1 Ein Wallfahrtslied. Gedenke, o HERR, dem David alle seine Mühen,
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2 daß er dem HERRN schwur und dem Mächtigen Jakobs gelobte:
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 Ich will nicht in das Zelt meines Hauses gehen, noch auf das Lager meines Bettes steigen,
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 ich will meinen Augen keinen Schlaf und meinen Augenlidern keinen Schlummer gönnen,
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 bis ich eine Stätte gefunden habe für den HERRN, eine Wohnung für den Mächtigen Jakobs!
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 Siehe, wir hörten, sie sei zu Ephrata; wir haben sie gefunden im Gefilde von Jear!
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 Wir wollen kommen zu seiner Wohnung, wir wollen anbeten beim Schemel seiner Füße!
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 HERR, mache dich auf zu deiner Ruhestatt, du und die Lade deiner Macht!
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 Deine Priester sollen sich in Gerechtigkeit kleiden, und deine Frommen sollen jubeln.
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 Um Davids, deines Knechtes willen weise nicht ab das Angesicht deines Gesalbten!
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 Der HERR hat David in Wahrheit geschworen, davon wird er nicht abgehen: «Von der Frucht deines Leibes will ich setzen auf deinen Thron!
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 Werden deine Söhne meinen Bund bewahren und meine Zeugnisse, die ich sie lehren will, so sollen auch ihre Söhne für immer sitzen auf deinem Thron!»
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 Denn der HERR hat Zion erwählt und sie zu seiner Wohnung begehrt:
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 «Dies ist für immer meine Ruhestatt, hier will ich wohnen; denn so habe ich es begehrt.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 Ihre Nahrung will ich reichlich segnen, ihre Armen sättigen mit Brot.
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 Ihre Priester will ich mit Heil bekleiden, und ihre Frommen sollen jubeln.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 Dort will ich dem David ein Horn hervorsprossen lassen, eine Leuchte zurichten meinem Gesalbten.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 Seine Feinde will ich mit Schande bekleiden; aber auf ihm soll seine Krone glänzen!»
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”