< Psalm 115 >
1 Nicht uns, HERR, nicht uns, sondern deinem Namen gib Ehre, um deiner Gnade und Treue willen!
Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
2 Warum sollen die Heiden sagen: «Wo ist denn ihr Gott?»
Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
3 Aber unser Gott ist ja im Himmel; er tut alles, was er will.
Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
4 Ihre Götzen sind Silber und Gold, von Menschenhänden gemacht.
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
5 Sie haben einen Mund und reden nicht, sie haben Augen und sehen nicht;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
6 Ohren haben sie und hören nicht, eine Nase haben sie und riechen nicht;
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
7 Hände haben sie und greifen nicht, Füße haben sie und gehen nicht; mit ihrer Kehle geben sie keinen Laut.
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
8 Ihnen sind gleich, die sie machen, alle, die auf sie vertrauen.
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
9 Israel, vertraue auf den HERRN! Er ist ihre Hilfe und ihr Schild.
Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
10 Haus Aaron, vertraue auf den HERRN! Er ist ihre Hilfe und ihr Schild.
Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
11 Die ihr den HERRN fürchtet, vertrauet auf den HERRN! Er ist ihre Hilfe und ihr Schild.
Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
12 Der HERR wolle unser gedenken; er wolle segnen! Er segne das Haus Israel, er segne das Haus Aaron!
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13 Er segne, die den HERRN fürchten, die Kleinen samt den Großen!
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14 Der HERR wolle euch mehren, euch und eure Kinder!
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
15 Gesegnet seid ihr vom HERRN, der Himmel und Erde gemacht hat.
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16 Der Himmel gehört dem HERRN; aber die Erde hat er den Menschenkindern gegeben.
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17 Die Toten rühmen den HERRN nicht und keiner, der zur Stille hinabfährt.
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18 Wir aber wollen den HERRN preisen von nun an bis in Ewigkeit. Hallelujah!
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.