< Psalm 109 >

1 Dem Vorsänger. Ein Psalm Davids. Gott, den ich rühme, schweige nicht!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 Denn sie haben ihr gottloses und falsches Maul wider mich aufgetan; sie sagen mir Lügen ins Gesicht,
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 sie bieten gehässige Worte über mich herum und bekämpfen mich ohne Grund.
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 Dafür, daß ich sie liebe, sind sie mir feind; ich aber bete.
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 Sie beweisen mir Böses für Gutes und Haß für Liebe.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Bestelle einen Gesetzlosen über ihn, und ein Ankläger stehe zu seiner Rechten!
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 Wenn er gerichtet wird, so möge er schuldig gesprochen werden, und sein Gebet werde ihm zur Sünde!
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 Seiner Tage seien wenige, und sein Amt empfange ein anderer!
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 Seine Kinder sollen Waisen werden und sein Weib eine Witwe!
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 Seine Kinder müssen umherwanken und betteln, hilfesuchend aus ihren Ruinen hervorkommen!
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 Der Gläubiger nehme ihm alles weg, und Fremde sollen plündern, was er sich erworben.
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 Niemand gebe ihm Gnadenfrist, und keiner erbarme sich seiner Waisen!
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 Seine Nachkommenschaft falle der Ausrottung anheim, ihr Name erlösche im zweiten Geschlecht!
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 Seiner Väter Missetat müsse gedacht werden vor dem HERRN, und seiner Mutter Sünde werde nicht ausgetilgt!
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 Der HERR habe sie beständig vor Augen, daß ihr Gedächtnis von der Erde vertilgt werde,
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 weil er nicht daran dachte, Barmherzigkeit zu üben, sondern den Elenden und Armen verfolgte und den Niedergeschlagenen, um ihn in den Tod zu treiben.
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 Da er den Fluch liebte, so komme er über ihn; und da er den Segen nicht begehrte, so sei er fern von ihm!
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 Er zog den Fluch an wie sein Gewand; so dringe er in sein Inneres wie Wasser und wie Öl in seine Gebeine;
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 er sei ihm wie das Kleid, das er anzieht, und wie der Gurt, damit er sich ständig umgürtet!
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Das sei der Lohn meiner Ankläger vonseiten des HERRN, derer, welche Arges wider meine Seele reden!
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 Du aber, o HERR, mein Herr, handle mit mir um deines Namens willen; denn deine Gnade ist gut; darum errette mich!
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Denn ich bin elend und arm, und mein Herz ist verwundet in meiner Brust.
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 Wie ein Schatten, wenn er sich neigt, schleiche ich dahin; ich werde verscheucht wie eine Heuschrecke.
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 Meine Knie wanken vom Fasten, mein Fleisch magert gänzlich ab;
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 und ich bin ihnen zum Gespött geworden; wer mich sieht, schüttelt den Kopf.
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Hilf mir, o HERR, mein Gott! Rette mich nach deiner Gnade,
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 so wird man erkennen, daß dies deine Hand ist, daß du, HERR, solches getan hast.
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 Fluchen sie, so segne du; setzen sie sich wider mich, so müssen sie zuschanden werden; aber dein Knecht müsse sich freuen.
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 Meine Ankläger müssen Schmach anziehen und in ihre Schande sich hüllen wie in einen Mantel.
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 Ich will den HERRN laut preisen mit meinem Munde und inmitten vieler ihn rühmen,
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 weil er dem Armen zur Seite steht, ihn zu retten von denen, die ihn verurteilen.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.

< Psalm 109 >