< Psalm 107 >
1 «Danket dem Herrn, denn er ist gütig, denn seine Gnade währt ewig!»
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 So sollen sagen die Erlösten des HERRN, die er aus der Hand des Feindes erlöst
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 und die er aus den Ländern zusammengebracht hat, vom Aufgang und vom Niedergang, von Mitternacht und vom Meer,
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 die irregingen in der Wüste, auf ungebahntem Weg und keine Stadt fanden, wo sie wohnen konnten,
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 hungrig und durstig, daß ihre Seele in ihnen verschmachtete.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Da schrieen sie zum HERRN in ihrer Not, und er rettete sie aus ihren Ängsten
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 und führte sie auf den rechten Weg, daß sie zu einer bewohnten Stadt gelangten,
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 die sollen dem HERRN danken für seine Gnade und für seine Wunder an den Menschenkindern,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 daß er die durstige Seele getränkt und die hungernde Seele mit Gutem gesättigt hat!
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Die in Finsternis und Todesschatten saßen, gebunden in Elend und Eisen,
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 weil sie den Geboten Gottes widerstrebt und den Rat des Höchsten verachtet hatten,
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 so daß er ihr Herz durch Strafe beugte, daß sie dalagen und ihnen niemand half.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Da schrieen sie zum HERRN in ihrer Not, und er rettete sie aus ihren Ängsten,
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 und führte sie aus Finsternis und Todesschatten heraus und zerriß ihre Bande,
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 die sollen dem HERRN danken für seine Gnade und für seine Wunder an den Menschenkindern,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 daß er eherne Türen zerbricht und eiserne Riegel zerschlägt!
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Die Toren, die wegen ihrer Übertretung und um ihrer Missetaten willen geplagt wurden,
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 daß ihrer Seele vor aller Nahrung ekelte und sie nahe waren den Pforten des Todes.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Da schrieen sie zum HERRN in ihrer Not, und er rettete sie aus ihren Ängsten.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Er sandte sein Wort und machte sie gesund und ließ sie ihren Gräbern entrinnen,
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 die sollen dem HERRN danken für seine Gnade und für seine Wunder an den Menschenkindern,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 sollen ihm Dankopfer bringen und seine Taten jubelnd erzählen!
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Die in Schiffen sich aufs Meer begaben und Handel trieben auf großen Wassern,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 die des HERRN Werke sahen und seine Wunder auf hoher See,
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 wenn er sprach und einen Sturmwind erregte, der die Wellen in die Höhe warf,
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 daß sie emporfuhren gen Himmel und hinabfuhren zur Tiefe und ihre Seele vor Angst verging;
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 daß sie wirbelten und schwankten wie Trunkene, und alle ihre Weisheit dahin war.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Da schrieen sie zum HERRN in ihrer Not, und er führte sie heraus aus ihren Ängsten;
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 er stillte den Sturm, daß er schwieg und die Wellen sich beruhigten;
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 und jene wurden froh, daß sie sich legten; und er führte sie an das erwünschte Gestade,
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 die sollen dem HERRN danken für seine Gnade und für seine Wunder an den Menschenkindern
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 und sollen ihn erheben in der Versammlung des Volkes und im Kreise der Ältesten ihn rühmen!
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Er machte Ströme zur Wüste und ließ Wasserquellen vertrocknen;
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 fruchtbares Land wurde zur Salzwüste wegen der Bosheit derer, die es bewohnten.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Er machte aber auch die Wüste zum Wasserteich und dürres Land zu Wasserquellen.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Und er ließ Hungrige daselbst wohnen, und sie gründeten eine bewohnte Stadt;
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 und sie säten Äcker an und pflanzten Weinberge und hatten von den Früchten einen schönen Ertrag;
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 und er segnete sie, daß sie sich stark mehrten, und auch ihres Viehs machte er nicht wenig,
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 nachdem sie vermindert worden waren und gedemütigt durch den Druck des Unglücks und Kummers,
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 als er Verachtung auf die Fürsten goß und sie irregehen ließ in unwegsamer Wildnis;
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 aber er erhob den Armen aus dem Elend und machte die Geschlechter wie Schafherden.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Die Redlichen sollen es sehen und sich freuen, und alle Bosheit soll ihr Maul verschließen!
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Wer weise ist, der beobachte solches und merke sich die Gnadenerweisungen des HERRN!
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.