< Psalm 103 >

1 Von David. Lobe den HERRN, meine Seele, und alles, was in mir ist, seinen heiligen Namen!
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
2 Lobe den HERRN, meine Seele, und vergiß nicht, was er dir Gutes getan!
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
3 Der dir alle deine Sünden vergibt und alle deine Gebrechen heilt;
wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
4 der dein Leben vom Verderben erlöst, der dich krönt mit Gnade und Barmherzigkeit;
wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
5 der dein Alter mit Gutem sättigt, daß du wieder jung wirst wie ein Adler.
Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
6 Der HERR übt Gerechtigkeit und schafft allen Unterdrückten Recht.
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7 Er hat seine Wege Mose kundgetan, den Kindern Israel seine Taten.
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8 Barmherzig und gnädig ist der HERR, geduldig und von großer Güte.
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9 Er wird nicht immerdar hadern und nicht ewiglich zürnen.
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10 Er hat nicht mit uns gehandelt nach unsern Sünden und uns nicht vergolten nach unsrer Missetat;
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11 denn so hoch der Himmel über der Erde ist, so groß ist seine Gnade über die, so ihn fürchten;
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12 so fern der Morgen ist vom Abend, hat er unsre Übertretung von uns entfernt.
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13 Wie sich ein Vater über Kinder erbarmt, so erbarmt sich der HERR über die, so ihn fürchten;
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
14 denn er weiß, was für ein Gemächte wir sind; er denkt daran, daß wir Staub sind.
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
15 Eines Menschen Tage sind wie Gras; er blüht wie eine Blume auf dem Felde;
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
16 wenn ein Wind darüber geht, so ist sie nimmer da, und ihre Stätte kennt sie nicht mehr;
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
17 aber die Gnade des HERRN währt von Ewigkeit zu Ewigkeit über die, so ihn fürchten, und seine Gerechtigkeit auf Kindeskind;
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
18 bei denen, die seinen Bund bewahren und an seine Gebote gedenken, sie zu tun.
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
19 Der HERR hat seinen Thron im Himmel gegründet, und seine Herrschaft erstreckt sich über alles.
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
20 Lobet den HERRN, ihr seine Engel, ihr starken Helden, die ihr seinen Befehl ausrichtet, gehorsam der Stimme seines Worts!
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
21 Lobet den HERRN, alle seine Heerscharen, seine Diener, die ihr seinen Willen tut!
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
22 Lobet den HERRN, alle seine Werke, an allen Orten seiner Herrschaft! Lobe den HERRN, meine Seele!
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.

< Psalm 103 >