< Psalm 102 >
1 Ein Gebet des Elenden, wenn er schmachtet und seine Klage vor dem HERRN ausschüttet. O HERR, höre mein Gebet, und mein Schreien komme vor dich!
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Verbirg dein Angesicht nicht vor mir am Tage meiner Not; neige dein Ohr zu mir; am Tage, da ich dich anrufe, erhöre mich eilends!
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Denn meine Tage sind in Rauch aufgegangen, und meine Gebeine glühen wie ein Ofen.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Mein Herz ist geschlagen und verdorrt wie Gras; denn ich habe vergessen, mein Brot zu essen.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Vor lauter Seufzen kleben meine Knochen an meinem Fleisch.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Ich gleiche einer Rohrdommel in der Wüste, bin wie ein Käuzlein in den Ruinen;
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 ich wache und bin wie ein einsamer Vogel auf dem Dach.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Täglich schmähen mich meine Feinde, und die wider mich toben, schwören bei mir;
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 denn ich esse Asche wie Brot und mische meinen Trank mit Tränen
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 wegen deines Grimms und deines Zorns, daß du mich aufgehoben und hingeschleudert hast.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Meine Tage sind wie ein langgestreckter Schatten, und ich verdorre wie Gras.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 Aber du, o HERR, bleibst ewig und dein Gedächtnis von einem Geschlecht zum andern.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Du wollest dich aufmachen und dich über Zion erbarmen; denn es ist Zeit, daß du ihr gnädig seiest, die Stunde ist gekommen!
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Denn deine Knechte lieben Zions Steine und trauern über ihren Schutt.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Dann werden die Heiden den Namen des HERRN fürchten und alle Könige auf Erden deine Herrlichkeit,
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 wenn der HERR Zion gebaut hat und erschienen ist in seiner Herrlichkeit,
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 wenn er sich zum Gebet der Heimatlosen gewendet und ihr Gebet nicht verachtet hat.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Das wird man aufschreiben für das spätere Geschlecht, und das Volk, das geschaffen werden soll, wird den HERRN loben,
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 daß er herabgeschaut hat von der Höhe seines Heiligtums, daß der HERR vom Himmel zur Erde geblickt hat,
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 zu hören das Seufzen der Gefangenen und loszumachen die Kinder des Todes;
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 auf daß sie den Namen des HERRN preisen zu Zion und sein Lob in Jerusalem,
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 wenn die Völker sich versammeln allzumal und die Königreiche, dem HERRN zu dienen.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 Er hat auf dem Wege meine Kraft gebeugt, meine Tage verkürzt.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Ich spreche: Mein Gott, nimm mich nicht weg in der Hälfte meiner Tage! Deine Jahre währen für und für.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Du hast vormals die Erde gegründet, und die Himmel sind deiner Hände Werk.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Sie werden vergehen, du aber bleibst; sie alle werden wie ein Kleid veralten, wie ein Gewand wirst du sie wechseln, und sie werden verschwinden.
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 Du aber bleibst, der du bist, und deine Jahre nehmen kein Ende!
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Die Kinder deiner Knechte werden bleiben, und ihr Same wird vor dir bestehen.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”