< Sprueche 5 >
1 Mein Sohn, merke auf meine Weisheit und neige dein Ohr meiner Belehrung zu;
Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
2 daß du Vorsicht übest und deine Lippen Erkenntnis bewahren.
don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
3 Denn von Honig triefen die Lippen der Fremden, und glätter als Öl ist ihr Gaumen;
Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
4 aber zuletzt ist sie bitter wie Wermut, scharf wie ein zweischneidig Schwert;
amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
5 ihre Füße laufen zum Tod, ihre Schritte streben dem Totenreich zu; (Sheol )
Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol )
6 den Pfad des Lebens erwägt sie nicht einmal; sie geht eine unsichere Bahn, die sie selbst nicht kennt.
Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
7 Und nun, ihr Söhne, höret mir zu und weichet nicht von den Reden meines Mundes!
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
8 Bleibe fern von dem Weg, der zu ihr führt, und nähere dich nicht der Tür ihres Hauses!
Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
9 Daß du nicht Fremden deine Ehre opferst und deine Jahre dem Grausamen;
don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
10 daß sich nicht Fremde von deinem Vermögen sättigen und du dich nicht abmühen müssest für eines andern Haus,
don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
11 also daß, wenn dir dann Leib und Fleisch hinschwindet, du zuletzt seufzen und sagen müssest:
A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
12 Warum habe ich doch die Zucht gehaßt, warum hat mein Herz die Zurechtweisung verachtet?
Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
13 Ich habe nicht gehört auf die Stimme meiner Lehrer und meinen Lehrmeistern kein Gehör geschenkt!
Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
14 Fast wäre ich gänzlich ins Unglück geraten, inmitten der Versammlung und der Gemeinde!
Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
15 Trinke Wasser aus deinem Born und Ströme aus deinem Brunnen!
Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
16 Sollen deine Quellen sich auf die Straße ergießen, deine Wasserbäche auf die Plätze?
In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
17 Sie sollen dir allein gehören und keinem Fremden neben dir!
Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
18 Dein Born sei gesegnet, und freue dich des Weibes deiner Jugend!
Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
19 Die liebliche Hindin, die anmutige Gemse, möge dich ihr Busen allezeit ergötzen, mögest du dich an ihrer Liebe stets berauschen!
Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
20 Warum aber, mein Sohn, wolltest du dich an einer andern vergehen und den Busen einer Fremden umarmen?
Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
21 Denn eines jeglichen Wege liegen klar vor den Augen des HERRN, und er achtet auf alle seine Pfade!
Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
22 Den Gottlosen nehmen seine eigenen Missetaten gefangen, und von den Stricken seiner Sünde wird er festgehalten.
Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
23 Er stirbt an Zuchtlosigkeit, und infolge seiner großen Torheit taumelt er dahin.
Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.