< Sprueche 3 >
1 Mein Sohn, vergiß meine Lehre nicht, und dein Herz bewahre meine Gebote!
Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
2 Denn sie werden dir Verlängerung der Tage und Jahre des Lebens und viel Frieden bringen.
gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
3 Gnade und Wahrheit werden dich nicht verlassen! Binde sie um deinen Hals, schreibe sie auf die Tafel deines Herzens,
Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 so wirst du Gunst und Wohlgefallen erlangen in den Augen Gottes und der Menschen.
Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
5 Vertraue auf den HERRN von ganzem Herzen und verlaß dich nicht auf deinen Verstand;
Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
6 erkenne ihn auf allen deinen Wegen, so wird er deine Pfade ebnen.
cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
7 Halte dich nicht selbst für weise; fürchte den HERRN und weiche vom Bösen!
Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
8 Das wird deinem Leib gesund sein und deine Gebeine erquicken!
Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
9 Ehre den HERRN mit deinem Gut und mit den Erstlingen all deines Einkommens,
Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
10 so werden sich deine Scheunen mit Überfluß füllen und deine Keltern von Most überlaufen.
ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
11 Mein Sohn, verwünsche nicht die Züchtigung des HERRN und laß dich seine Strafe nicht verdrießen;
Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
12 denn welchen der HERR lieb hat, den züchtigt er, wie ein Vater den Sohn, dem er wohlwill.
domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
13 Wohl dem Menschen, der Weisheit findet, dem Menschen, der Verstand bekommt!
Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
14 Denn ihr Erwerb ist besser als Gelderwerb, und ihr Gewinn geht über feines Gold.
gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
15 Sie ist kostbarer als Perlen, und alle deine Schätze sind ihr nicht zu vergleichen.
Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
16 In ihrer Rechten ist langes Leben, in ihrer Linken Reichtum und Ehre.
Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
17 Ihre Wege sind liebliche Wege und alle ihre Pfade Frieden.
Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
18 Sie ist ein Baum des Lebens denen, die sie ergreifen; und wer sie festhält, ist glücklich zu preisen.
Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
19 Der HERR hat die Erde mit Weisheit gegründet und die Himmel mit Verstand befestigt.
Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
20 Durch seine Erkenntnis brachen die Fluten hervor und träufelten die Wolken Tau.
ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
21 Solches, mein Sohn, laß niemals aus den Augen; bewahre Überlegung und Besonnenheit!
Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
22 Sie werden deiner Seele zum Leben dienen und zum Schmuck deinem Hals.
za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
23 Dann wirst du sicher deines Weges gehen, und dein Fuß stößt nicht an.
Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
24 Ohne Furcht wirst du dich niederlegen, und liegst du, so wird dein Schlaf süß sein.
sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
25 Du brauchst keinen plötzlichen Schrecken zu fürchten, auch nicht den Untergang der Gottlosen, wenn er kommt.
Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
26 Denn der HERR wird in deinem Herzen sein und deinen Fuß bewahren vor dem Fallstrick.
gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
27 Verweigere keinem Bedürftigen eine Wohltat, wenn es in deiner Hände Macht steht, sie zu erweisen!
Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
28 Sprich nicht zu deinem Nächsten: «Gehe hin und komme wieder; morgen will ich dir geben!» während du es doch hast.
Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
29 Ersinne nichts Böses wider deinen Nächsten, der arglos bei dir wohnt.
Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
30 Hadere mit keinem Menschen ohne Ursache, wenn er dir nichts Böses zugefügt hat.
Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
31 Sei nicht neidisch auf den Gewalttätigen und erwähle dir keinen seiner Wege!
Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
32 Denn der Verkehrte ist dem HERRN ein Greuel, aber mit Aufrichtigen ist er vertraut.
Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
33 Der Fluch des HERRN ist im Hause des Gottlosen, aber die Wohnung der Gerechten segnet er.
La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
34 Wenn er der Spötter spottet, so gibt er den Demütigen Gnade.
Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
35 Die Weisen ererben Ehre, die Toren aber macht die Schande berühmt.
Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.