< Sprueche 24 >

1 Beneide böse Menschen nicht und begehre nicht, es mit ihnen zu halten;
Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
2 denn ihr Herz trachtet nach Schaden, und ihre Lippen reden Unheil!
gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
3 Durch Weisheit wird ein Haus gebaut, und durch Verstand wird es sich behaupten;
Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
4 auch werden durch Einsicht seine Kammern mit allerlei köstlichem und lieblichem Gut gefüllt.
ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
5 Ein weiser Mann ist stark, und ein verständiger Mensch stählt seine Kraft.
Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
6 Denn durch kluge Maßregeln gewinnst du die Schlacht und durch die Menge der Ratgeber den Sieg.
don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
7 Die Weisheit ist dem Narren zu hoch; er tut seinen Mund nicht auf im Tor!
Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
8 Wer vorsätzlich Böses tut, den nenne man einen Bösewicht!
Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
9 Dummheiten ersinnen ist Sünde, und ein Spötter ist ein abscheulicher Mensch!
Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
10 Zeigst du dich schwach am Tage der Not, so ist deine Kraft beschränkt!
In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
11 Errette, die zum Tode geschleppt werden, und die zur Schlachtbank wanken, halte zurück!
Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
12 Wenn du sagen wolltest: «Siehe, wir haben das nicht gewußt!» wird nicht der, welcher die Herzen prüft, es merken, und der deine Seele beobachtet, es wahrnehmen und dem Menschen vergelten nach seinem Tun?
In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
13 Iß Honig, mein Sohn, denn er ist gut, und Honigseim ist süß für deinen Gaumen!
Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
14 So erkenne auch, daß die Weisheit gut ist für deine Seele; wenn du sie gefunden hast, so hast du eine Zukunft, und deine Hoffnung wird nicht vernichtet werden.
Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
15 Du Gottloser, laure nicht auf die Wohnung des Gerechten und störe seine Ruhe nicht!
Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
16 Denn der Gerechte fällt siebenmal und steht wieder auf; aber die Gottlosen stürzen nieder im Unglück.
gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
17 Freue dich nicht über den Fall deines Feindes, und wenn er strauchelt, so frohlocke nicht!
Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
18 daß nicht der HERR es sehe und es ihm mißfalle und er seinen Zorn abwende von ihm.
in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
19 Erzürne dich nicht über die Bösen, sei nicht neidisch auf die Übeltäter!
Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
20 Denn der Böse hat keine Zukunft, und die Leuchte der Gottlosen wird erlöschen.
gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
21 Fürchte den HERRN, mein Sohn, und den König, und laß dich nicht mit Neuerungssüchtigen ein!
Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
22 Denn ihr Unglück wird plötzlich kommen und ihrer beider Verderben; wer kennt es?
gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
23 Auch diese Sprüche kommen von den Weisen: die Person ansehen im Gericht, ist nicht gut.
Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
24 Wer zum Gottlosen spricht: «Du bist gerecht!» dem fluchen die Völker, und die Leute verwünschen ihn;
Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
25 aber an denen, die recht richten, hat man Wohlgefallen, und über sie kommt der Segen des Guten.
Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
26 Eine rechte Antwort ist wie ein Kuß auf die Lippen.
Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
27 Verrichte zuerst draußen dein Geschäft und besorge deine Feldarbeit, darnach baue dein Haus.
Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
28 Tritt nicht ohne Ursache als Zeuge auf wider deinen Nächsten! Was willst du irreführen mit deinen Lippen?
Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
29 Sage nicht: «Wie er mir getan, so will ich ihm tun; ich will dem Mann vergelten nach seinem Werk!»
Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
30 Ich ging vorüber an dem Acker des Faulen und an dem Weinberge des Unverständigen
Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
31 und siehe, er ging ganz in Disteln auf, und Nesseln überwucherten ihn, und seine Mauer war eingestürzt.
ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
32 Das sah ich und nahm es zu Herzen; ich betrachtete es und zog eine Lehre daraus:
Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
33 «Ein wenig schlafen, ein wenig schlummern, die Hände ein wenig ineinanderlegen, um zu ruhen»;
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
34 so kommt deine Armut wie ein Landstreicher dahergeschritten und dein Mangel wie ein gewappneter Mann!
sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.

< Sprueche 24 >