< Klagelieder 3 >

1 Ich bin der Mann, der tief gebeugt worden ist durch die Rute seines Zorns.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Mich hat er verjagt und in die Finsternis geführt und nicht ans Licht.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Nur gegen mich kehrt er immer wieder den ganzen Tag seine Hand.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Er hat mein Fleisch und meine Haut verschlungen und meine Knochen zermalmt.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 Er hat rings um mich her Gift und Drangsal aufgebaut.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 In dunkeln Höhlen läßt er mich wohnen wie längst Verstorbene.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Er hat mich eingemauert, daß ich nicht herauskommen kann; mit ehernen Ketten hat er mich beschwert.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Ob ich auch schreie und rufe, verstopft er doch die Ohren vor meinem Gebet.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 Quadersteine legt er mir in den Weg, krümmt meine Pfade.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Er lauert mir auf wie ein Bär, wie ein Löwe im Dickicht.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 Er hat mich auf Abwege gebracht, ist über mich hergefallen und hat mich arg zugerichtet.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 Er hat seinen Bogen gespannt und mich dem Pfeile zum Ziel gesetzt.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 Er hat mir seines Köchers Söhne in die Nieren gejagt.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 Ich bin allem Volk zum Gelächter geworden, ihr Liedlein den ganzen Tag.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 Er hat mich mit Bitterkeit gesättigt, mit Wermut getränkt.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 Er ließ meine Zähne sich an Kies zerbeißen, er hat mich mit Asche bedeckt.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 Und du hast meine Seele aus dem Frieden verstoßen, daß ich des Glückes vergaß.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 Und ich sprach: Meine Lebenskraft ist dahin, meine Hoffnung auf den HERRN.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Sei eingedenk meines Elends, meiner Verfolgung, des Wermuts und des Gifts!
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Beständig denkt meine Seele daran und ist tief gebeugt!
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Dieses aber will ich meinem Herzen vorhalten, darum will ich Hoffnung fassen:
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Gnadenbeweise des HERRN sind's, daß wir nicht gänzlich aufgerieben wurden, denn seine Barmherzigkeit ist nicht zu Ende;
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 sie ist alle Morgen neu, und deine Treue ist groß!
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 Der HERR ist mein Teil, spricht meine Seele; darum will ich auf ihn hoffen.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Der HERR ist gütig gegen die, welche auf ihn hoffen, gegen die Seele, die nach ihm fragt.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 Gut ist's, schweigend zu warten auf das Heil des HERRN.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 Es ist einem Manne gut, in seiner Jugend das Joch zu tragen.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Er sitze einsam und schweige, wenn man ihm eines auferlegt!
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Er stecke seinen Mund in den Staub; vielleicht ist noch Hoffnung vorhanden!
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Schlägt ihn jemand, so biete er ihm den Backen dar und lasse sich mit Schmach sättigen!
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Denn der Herr wird nicht ewig verstoßen;
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 sondern wenn er betrübt hat, so erbarmt er sich auch nach der Größe seiner Gnade.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 Denn nicht aus Lust plagt und betrübt ER die Menschenkinder.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 Wenn alle Gefangenen eines Landes mit Füßen getreten,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 wenn das Recht eines Mannes vor dem Angesicht des Höchsten gebeugt,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 die Rechtssache eines Menschen verdreht wird, sollte der Herr es nicht beachten?
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Wer hat je etwas gesagt und es ist geschehen, ohne daß der Herr es befahl?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Geht nicht aus dem Munde des Höchsten das Böse und das Gute hervor?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Was beklagt sich der Mensch? Es hätte sich wahrlich jeder über seine Sünde zu beklagen!
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Lasset uns unsere Wege erforschen und durchsuchen und zum HERRN zurückkehren!
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Lasset uns unsere Herzen samt den Händen zu Gott im Himmel erheben!
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 Wir sind abtrünnig und widerspenstig gewesen; das hast du nicht vergeben;
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 du hast dich im Zorn verborgen und uns verfolgt; du hast uns ohne Gnade erwürgt;
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 du hast dich in eine Wolke gehüllt, daß kein Gebet hindurchdrang;
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 du hast uns zu Kot und Abscheu gemacht unter den Völkern!
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 Alle unsere Feinde haben ihr Maul gegen uns aufgesperrt.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Grauen und Grube wurden uns beschieden, Verwüstung und Untergang.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Es rinnen Wasserbäche aus meinen Augen wegen des Untergangs der Tochter meines Volkes.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Mein Auge tränt unaufhörlich; denn da ist keine Ruhe,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 bis der HERR vom Himmel herabschauen und dareinsehen wird.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Was ich sehen muß, tut meiner Seele weh ob aller Töchter meiner Stadt.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Die mich ohne Ursache hassen, stellten mir heftig nach wie einem Vogel;
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 sie wollten mich in der Grube ums Leben bringen und warfen Steine auf mich.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Die Wasser gingen über mein Haupt; ich sagte: Ich bin verloren!
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Aber ich rief, HERR, deinen Namen an, tief unten aus der Grube.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Du hörtest meine Stimme: «Verschließe dein Ohr nicht vor meinem Seufzen, vor meinem Hilferuf!»
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Du nahtest dich mir des Tages, als ich dich anrief, du sprachest: Fürchte dich nicht!
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Du führtest, o Herr, die Sache meiner Seele, du rettetest mir das Leben!
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Du hast, o HERR, meine Unterdrückung gesehen; schaffe du mir Recht!
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Du hast all ihre Rachgier gesehen, alle ihre Anschläge wider mich;
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 du hast, o HERR, ihr Schmähen gehört, alle ihre Pläne gegen mich,
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 die Reden meiner Widersacher und ihr beständiges Murmeln über mich.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Siehe doch: ob sie niedersitzen oder aufstehen, so bin ich ihr Spottlied.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Vergilt ihnen, o HERR, nach dem Werk ihrer Hände!
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Gib ihnen Verstockung ins Herz, dein Fluch komme über sie!
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Verfolge sie in deinem Zorn und vertilge sie unter dem Himmel des HERRN hinweg!
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Klagelieder 3 >