< Job 9 >

1 Da antwortete Hiob und sprach:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Wahrhaftig, ich weiß, daß dem so ist; und wie kann der schwache Mensch rechten mit dem starken Gott!
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 Wollte er mit Ihm rechten, so könnte er Ihm auf tausend nicht eins beantworten.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Er ist weisen Herzens und von ungebrochener Kraft; wer hat ihm je getrotzt und es durchgesetzt?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 Er verrückt Berge, und man merkt es nicht, daß er sie in seinem Zorn umgekehrt hat.
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 Er bewegt die Erde von ihrem Ort, daß ihre Säulen zittern.
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 Er gebietet der Sonne, so geht sie nicht auf; er legt die Sterne unter Siegel.
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 Er allein spannt den Himmel aus und tritt auf Meereswogen daher.
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 Er macht den Bären, den Orion und das Siebengestirn, samt den Kammern des Südens.
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 Er tut große Dinge, die unerforschlich sind, Wunder ohne Zahl.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Siehe, er geht an mir vorüber, und ich sehe ihn nicht; er fährt vorbei, und ich gewahre ihn nicht.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Er rafft dahin, wer hindert ihn? Wer ruft ihm zu: Was machst du da?
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 Gott unterdrückt nicht seinen Zorn; Rahabs Helfer beugen sich unter ihn.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 Wie sollte ich ihm denn antworten und Worte finden, um mit ihm zu reden?
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 Auch wenn ich im Recht wäre, dürfte ich ihm nicht entgegnen; ich müßte meinen Richter um Gnade anflehen.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Wenn ich rufe, wird er mir antworten? Ich glaube nicht, daß er meine Stimme hört;
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 denn im Sturm hat er mich zerschlagen und mir ohne Ursache viele Wunden zugefügt.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 Er läßt mich nicht einmal Atem holen, sondern sättigt mich mit Bitterkeit.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 Kommt's auf die Kraft an, siehe, so ist er stark; wenn aber aufs Recht, wer ladet mich dann vor?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Wenn ich schon im Recht bin, so wird mich doch mein Mund verdammen, und bin ich auch unschuldig, so kommt es doch verkehrt heraus.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 Ich bin unschuldig, bin unbesorgt um meine Seele; ich verachte das Leben!
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 Darum sage ich: Es ist einerlei; Fromme und Gottlose bringt er gleicherweise um!
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 Wenn die Geißel plötzlich tötet, so lacht er der Prüfung der Unschuldigen.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 Die Erde ist in die Gewalt des Frevlers gegeben; das Angesicht ihrer Richter verhüllt er; wenn nicht er, wer tut es denn?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 Meine Tage eilen schneller dahin als ein Läufer; sie sind entflohen und haben nichts Gutes gesehen;
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 sie sind vorbeigefahren wie Rohrschiffe, wie ein Adler, der sich auf Beute stürzt.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 Wenn ich denke: Ich will meiner Klage vergessen, meine Miene ändern und heiter dreinschauen,
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 so muß ich meine vielen Schmerzen fürchten; denn ich weiß, daß du mich nicht lossprechen wirst!
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 Soll ich denn schuldig sein, was mühe ich mich vergeblich ab?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 Wüsche ich mich auch mit Schnee und reinigte meine Hände mit Lauge,
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 so würdest du mich doch in die Grube tauchen, daß ich meine Kleider nicht mehr anziehen dürfte!
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 Denn er ist nicht ein Mann wie ich, daß ich ihm antworten könnte, daß wir miteinander vor Gericht gingen;
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 es ist auch kein Schiedsrichter zwischen uns, der seine Hand auf uns beide legen könnte.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Er nehme aber seine Rute von mir, und sein Schrecken überfalle mich nicht,
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 so will ich reden und ihn nicht fürchten; denn nicht also steht es in mir selbst.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Job 9 >