< Job 36 >

1 Und Elihu fuhr fort und sprach:
Elihu ya ci gaba,
2 Gedulde dich noch ein wenig, so will ich dich lehren, ich habe noch mehr zu reden für Gott.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 Ich will mein Wissen weither holen und meinem Schöpfer Gerechtigkeit widerfahren lassen!
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 Denn wahrlich, meine Reden sind keine Lügen, du hast es mit einem ganz Verständigen zu tun!
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Siehe, Gott ist mächtig, doch verachtet er niemand; groß ist die Kraft seines Herzens.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 Den Gottlosen läßt er nicht leben, aber den Elenden schafft er Recht.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 Er wendet seine Augen nicht ab von den Gerechten und setzt sie auf ewig mit Königen auf den Thron, damit sie herrschen.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 Sind sie aber in Fesseln gebunden, in Banden des Elends gefangen,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 so hält er ihnen ihre Taten und ihre Übertretungen vor; denn sie haben sich überhoben;
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 er öffnet ihr Ohr der Bestrafung und befiehlt ihnen, sich von der Bosheit abzukehren.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 Wenn sie dann gehorchen und sich unterwerfen, so werden sie ihre Tage in Glück und ihre Jahre in Wohlfahrt beendigen.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 Gehorchen sie aber nicht, so kommen sie um durchs Schwert und sterben dahin in ihrem Unverstand.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 Denn die, welche ruchlosen Herzens sind, widersetzen sich; sie flehen nicht, wenn er sie gefesselt hat.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 Ihre Seele stirbt in der Jugend und ihr Leben unter den Hurern.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 Den Gedemütigten aber rettet er durch die Demütigung und öffnet durch die Trübsal sein Ohr.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 Und auch dich lockt er aus der Enge in die Weite, da keine Not mehr sein wird, und an einen reichbesetzten Tisch.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 Bist du aber vom Urteil des Gottlosen erfüllt, so werden Urteil und Gericht dich treffen.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Der Zorn verleite dich ja nicht zur Lästerung, und die Menge des Lösegeldes besteche dich nicht.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Wird er deinen Reichtum schätzen? Er achtet nicht auf Gold, noch auf alle Anstrengungen der Kraft.
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Sehne dich nicht nach der Nacht, da Völker untergehen werden.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Hüte dich, wende dich nicht zum Bösen, denn dieses ziehst du dem Leiden vor.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Siehe, Gott ist erhaben in seiner Kraft, wo ist ein Lehrer wie er?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Wer will ihn zur Rede stellen über seinen Weg, und wer will zu ihm sagen: Du hast Unrecht getan?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Gedenke daran, sein Tun zu erheben; die Menschen sollen es besingen.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 Alle Menschen sehen es ja, der Sterbliche schaut es von ferne.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Siehe, wie erhaben ist Gott! Wir aber verstehen ihn nicht; die Zahl seiner Jahre hat niemand erforscht.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 Denn er zieht Wassertropfen herauf; sie träufeln als Regen aus seinem Dunst, den die Wolken rieseln lassen,
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 sie triefen auf viele Menschen herab.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 Versteht man auch das Ausspannen der Wolken und das Krachen seines Gezelts?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Siehe, er breitet sein Licht um sich her aus und bedeckt die Gründe des Meeres;
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 denn damit richtet er die Völker und gibt Speise die Fülle.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 Seine Hände bedeckt er mit Licht und gebietet ihm, zu treffen.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 Sein Donnern kündigt ihn an, die Herde sein Heraufsteigen [im Gewitter].
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.

< Job 36 >