< Job 26 >
1 Und Hiob antwortete und sprach:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Wie hast du doch den Ohnmächtigen unterstützt und dem machtlosen Arm geholfen!
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 Wie hast du den Unweisen beraten und Weisheit in Fülle kundgetan!
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 Wen hast du mit deiner Rede getroffen und wessen Odem ging aus deinem Munde hervor?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 Die Schatten werden von Zittern erfaßt unter den Wassern und ihren Bewohnern.
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 Das Totenreich ist enthüllt vor Ihm, und der Abgrund hat keine Decke. (Sheol )
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol )
7 Er spannt den Norden aus über der Leere und hängt die Erde über dem Nichts auf.
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 Er bindet die Wasser in seinen Wolken zusammen, und das Gewölk zerbricht nicht unter ihrem Gewicht.
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 Er verschließt den Anblick seines Thrones, er breitet seine Wolken darüber.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 Er hat einen Kreis abgesteckt auf der Oberfläche der Wasser, zur Grenze des Lichts und der Finsternis.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 Des Himmels Säulen erbeben und zittern vor seinem Schelten.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 Durch seine Kraft erregt er das Meer, und mit seinem Verstand zerschlägt er das Ungeheuer.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 Durch seinen Hauch wird der Himmel klar, mit seiner Hand durchbohrt er die flüchtige Schlange.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Siehe, das sind die Umrisse seiner Wege; wie leise ist das Wort, das wir davon vernehmen! Wer will aber den Donner seiner Macht verstehen?
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”