< Job 25 >

1 Da antwortete Bildad, der Schuchiter, und sprach:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Herrschaft und Schrecken sind bei Ihm; Frieden schafft Er in seinen Höhen.
“Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
3 Sind seine Scharen zu zählen? Und über wem erhebt sich nicht sein Licht?
Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
4 Wie kann aber der Sterbliche gerecht sein vor Gott, und wie will der rein sein, der vom Weibe geboren ist?
Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
5 Siehe, sogar der Mond leuchtet nicht helle, und die Sterne sind nicht rein vor ihm,
In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
6 wie viel weniger der Sterbliche, der Wurm, und das Menschenkind, das nur ein Würmlein ist?
mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”

< Job 25 >