< Psalm 85 >
1 Dem Musikmeister; von den Korahiten ein Psalm. Du hast zwar, HERR, deinem Lande Gnade gewährt,
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ka nuna wa ƙasarka alheri, ya Ubangiji; ka mai da nasarorin Yaƙub.
2 hast deinem Volke die Schuld vergeben und all seine Sünde zugedeckt, (SELA)
Ka gafarta laifin mutanenka ka kuma shafe dukan zunubansu. (Sela)
3 hast deinem ganzen Groll entsagt, von der Glut deines Zorns dich abgewandt:
Ka kau da dukan fushinka ka kuma juye daga hasalar fushinka.
4 stell uns nun aber auch wieder her, du Gott unsers Heils, und laß deinen Unmut gegen uns schwinden!
Ka sāke mai da mu, ya Allah Mai Cetonmu, ka kau da rashin jin daɗinka daga gare mu.
5 Willst du denn unversöhnlich gegen uns zürnen und deinen Zorn fortdauern lassen für und für?
Za ka ci gaba da fushi da mu har abada ne? Za ka ja fushinka cikin dukan tsararraki?
6 Willst du uns nicht wieder neu beleben, daß dein Volk sich deiner mag freuen?
Ba za ka sāke raya mu ba, don mutanenka su yi farin ciki a cikinka?
7 Laß uns schauen, o HERR, deine Gnade und gewähre uns dein Heil!
Ka nuna mana ƙaunarka marar ƙarewa, ya Ubangiji, ka kuma ba mu cetonka.
8 Ich will doch hören, was Gott der HERR verkündet! – Fürwahr, er kündet Segen an seinem Volke und seinen Frommen; nur daß sie nicht wieder sich wenden zur Torheit!
Zan saurari abin da Allah Ubangiji zai faɗa; ya yi alkawarin salama ga mutanensa, tsarkakansa, amma kada su koma ga wauta.
9 Wahrlich, sein Heil ist denen nah, die ihn fürchten, daß Herrlichkeit in unserm Lande wohne,
Tabbatacce cetonsa yana kusa da waɗanda suke tsoronsa, don ɗaukakarsa ta zauna a cikin ƙasarmu.
10 daß Gnade und Treue einander begegnen, Gerechtigkeit und Friede sich küssen.
Ƙauna da aminci za su sadu; adalci da salama za su yi wa juna sumba.
11 Die Treue wird aus der Erde sprossen und Gerechtigkeit vom Himmel niederschauen.
Aminci zai ɓulɓulo daga ƙasa, adalci kuma yă duba daga sama.
12 Dann wird uns der HERR auch Segen spenden, daß unser Land uns seinen Ertrag gewährt;
Ubangiji tabbatacce zai bayar da abin da yake da kyau, ƙasarmu kuwa za tă ba da amfaninta.
13 Gerechtigkeit wird vor ihm hergehn und achten auf den Weg seiner Schritte.
Adalci na tafiya a gabansa yana shirya hanya domin ƙafafunsa.